< Yoshuwa 16 >
1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
Soge amo da Yousefe egaga fi ilima ilegei da agoane. Ga (south) alalo da Yodane Hano amo Yeligou moilai bai bagade gadenene ba: i. Alalo da Yeligou Bubuga: su hano amo eso mabadi la: idi ba: i. Amoga asili alalo da wadela: i sogega asili, agolo sogega asili, Bedele moilaiga doaga: i.
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
Bedele moilai baligili, alalo da Lase moilaiga asili A: dalode A: da moilaiga doaga: i. (Agaide dunu da amo moilaiga esalu.)
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
Amalu, alalo da eso dabe la: idi amoga asili Ya: felidaide dunu ilia soge Bede Holone soge amo ganodini doaga: i. Amalu, ilia soge alalo da Gisa soge baligili, Medidela: inia Hano Wayabo amoga doaga: i.
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
Yousefe egaga fi (Ifala: me fi amola Eso Dabe Ma: na: se fi) da amo soge lai dagoi.
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
Ifala: ime fi dunu ilia soge alalo da A: dalode A: da amoga eso mabadi la: idi asili gadodili Bede Houlone baligili,
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
Medidela: inia Hano Wayabo Bagade amoga doaga: i. Migimida moilai da ilia sogega gano ba: i. Eso mabadi la: ididili, alalo da selefale asili Da: ina: de Siailou eso mabadi la: ididili baligili, Yanoua moilaiga doaga: i.
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
Amoga asili, alalo da A: dalode amola Na: iala baligili, Yeligou moilai bai bagade amola Yodane Hano doaga: i.
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
Alalo da eso dabe la: idi amo Dabua fisili, Gana Hano amoga asili, Medidela: inia Hano amoga doaga: i.
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
Ifala: ime fi da amo soge lai. Amola ilia da moilai afae afae amo Eso Dabe Ma: na: se fi ilia soge alalo ganodini amo lai dagoi.
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
Be ilia da Ga: ina: ne fi dunu Gisa soge amo ganodini esalu, amo gadili hame sefasi. Amaiba: le, Ga: ina: ne fi dunu da Ifala: ime fi amo ganodini wali esala. Be ilia da udigili bidi mae lawane hawa: hamosu dunu esala.