< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
La parte que le tocó en suerte a la tribu de los hijos de Judá, según sus familias, iba hacia el límite de Edom, hacia el desierto de Zin al extremo sur.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
Su límite por el lado sur iba desde la costa del mar Salado, desde la bahía que mira hacia el sur,
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
y seguía por el sur hacia la subida de Acrabim, pasaba hasta Zin, subía por el sur de Cades Barnea y pasaba por Hebrón, y después de subir por Adar, volvía a Carca.
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
De allí pasaba a Asmón y seguía hasta el arroyo de Egipto, y terminaba en el mar. Éste les será el límite del sur.
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
El límite oriental era el mar Salado hasta la desembocadura del Jordán. El límite del norte era desde la costa del mar en la desembocadura del Jordán,
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
y el lindero subía a Bet-hogla, pasaba al norte de Bet-arabá y subía hasta la piedra de Bohán, hijo de Rubén.
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
El lindero subía después desde el valle de Acor hasta Debir, y por el norte volvía hacia Gilgal, que se encuentra frente a la subida de Adumim, situada al lado sur del valle. Después el límite pasaba por las aguas de En-semes, y terminaba en En-rogel.
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
El lindero subía por el valle del hijo de Hinom, en el lado sur de donde estaban los jebuseos, es decir, Jerusalén, y subía a la cumbre de la montaña que está delante del valle de Hinom hacia el occidente, en el extremo norte del valle de Refaim.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
Desde la cumbre de la montaña el límite volvía hasta la fuente de las aguas de Neftoa, y salía a las ciudades de la montaña Efrón, luego rodeaba a Baala, la cual es Quiriat-jearim.
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
De Baala el límite giraba al occidente hasta la montaña Seír, y pasaba por la ladera de la montaña Jearim, por el norte, que es Quesalón, y descendía a Bet-semes, y pasaba a Timná.
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
Después la línea partía hacia la ladera de Ecrón, al norte, y giraba hacia Sicrón y después de pasar por la montaña Baala, salía a Jabneel, y el límite terminaba en el mar.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
El límite occidental era el mar Grande. Estos son los límites alrededor de los hijos de Judá, según sus familias.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
Pero a Caleb, hijo de Jefone, le dio su porción entre los hijos de Judá, conforme a la Palabra de Yavé [dada] a Josué, la ciudad de Arba, padre de Anac, la cual es Hebrón.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
Caleb echó de allí a tres de los hijos de Anac: a Sesai, Aimán y Talmai, descendientes de Anac.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
De allí subió contra los habitantes de Debir. Antiguamente el nombre de Debir era Quiriat-séfer.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
Entonces Caleb dijo: Al que ataque a Quiriat-sefer, y la conquiste, le daré a mi hija Acsa como esposa.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
Otoniel, hijo de Cenaz, hermano de Caleb, la conquistó. Y él le dio como esposa a su hija Acsa.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
Aconteció que cuando la llevaba, él la incitó a que pidiera a su padre un campo. Ella desmontó del asno, por lo cual Caleb le dijo: ¿Qué quieres?
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
Ella entonces respondió: Dame una bendición. Porque me diste una tierra de sequedal, dame también fuentes de agua. Y él le dio las fuentes de arriba y las fuentes de abajo.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
Esta es la heredad de la tribu de los hijos de Judá, según sus familias.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
Las ciudades en el extremo sur de la tribu de los hijos de Judá, hacia el límite de Edom, fueron Cabseel, Eder, Jagur,
22 Kina, Dimona, Adada,
Cina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
Cedes, Hazor, Itnán,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Zif, Telem, Bealot,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
Hazor-hadata, Queriot, Hesrón (que es Hazor),
26 Amam, Shema, Molada,
Amam, Sema, Molada,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
Hazar-gada, Hesmón, Bet-pelet,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
Hazar-sual, Beerseba, Bizotia,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
Baala, Lim, Esem,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
Eltolad, Quesil, Horma,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
Siclag, Madmana, Sansana,
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
Lebaot, Silim, Aín y Rimón: 29 ciudades con sus aldeas.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
En la llanura: Estaol, Sora, Asena,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
Zanoa, Enganim, Tapúa, Enam,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Jerimut, Adulam, Soco, Azeca,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
Saraim, Aditaim, Gedera y Gederotaim: 14 ciudades con sus aldeas.
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
Zenán, Hadasa, Migdal-gad,
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
Dileán, Mizpa, Jocteel,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Laquis, Boscat, Eglón,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
Cabón, Lahmam, Quitlis,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Gederot, Bet-dagón, Naama y Maceda: 16 ciudades con sus aldeas.
42 Libna, Eter, Ashan,
Libná, Eter y Asán,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
Jifta, Asena y Nezib,
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Queila, Aczib y Maresa: nueve ciudades con sus aldeas.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Ecrón con sus villas y sus aldeas.
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
Desde Ecrón hasta el mar, todas las que están junto a Asdod, con sus aldeas.
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Asdod, sus villas y sus aldeas. Gaza, sus villas y sus aldeas hasta el río de Egipto y el mar Grande, con su territorio.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
En la región montañosa: Samir, Jatir, Sucot,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
Dana, Quiriat-sana, que es Debir,
50 Anab, Eshtemo, Anim,
Anab, Estemó, Anim,
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
Gosén, Holón y Gilo: 11 ciudades con sus aldeas.
52 Arab, Duma, Eshan,
Arab, Duma, Esán,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
Janum, Bet-tapúa, Afeca,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Humta, Quiriat-arba, que es Hebrón, y Sior: nueve ciudades con sus aldeas.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maón, Carmel, Zip, Juta,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
Izreel, Jocdeam, Zanoa,
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Caín, Gabaa y Timná: diez ciudades con sus aldeas.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul, Bet-sur, Gedor,
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Maarat, Bet-anot y Eltecón: seis ciudades con sus aldeas.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Quiriat-baal, que es Quiriat-jearim, y Rabá: dos ciudades con sus aldeas.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
En el desierto: Bet-arabá, Midín, Secaca,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Nibsán, la Ciudad de la Sal, y En-guedi: seis ciudades con sus aldeas.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
Pero los hijos de Judá no pudieron echar a los jebuseos que habitaban en Jerusalén. Así que los jebuseos viven con los hijos de Judá en Jerusalén hasta hoy.

< Yoshuwa 15 >