< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
Esta fue la tierra asignada a la tribu de Judá, por familias: se extendía hacia el sur hasta la frontera de Edom, hasta el desierto de Zin en el extremo sur.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
Su frontera comenzaba en el extremo del Mar Salado – la bahía que mira hacia el sur —
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
Hai luego iba hacia el sur del Paso de los escorpiones, a través del desierto de Zin, para luego dirigirse al sur de Cades-barnea hasta Hezrón. Desde allí subía hasta Adar y luego giraba hacia Carca,
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
pasando por Azmon y saliendo al Wadi de Egipto, terminando en el mar. Esta era su frontera sur.
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
La frontera oriental de Judá era el Mar Salado, hasta donde termina el río Jordán. El límite septentrional iba desde la bahía septentrional del mar donde termina el Jordán,
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
hasta el límite de Bet-Joglá, y luego al norte de Bet-arabá hasta la Piedra de Bohán (hijo de Rubén).
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
Desde allí iba hasta el límite de Debir por el valle de Acor, y giraba al norte hacia Gilgal, frente a las alturas de Adumín, al sur del valle. Luego el límite continuaba hasta las aguas de En-semes y hasta En-rogel.
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
El límite pasaba entonces por el valle de Ben-Hinón, a lo largo de la ladera sur de los jebuseos, (es decir, Jerusalén), y luego subía a la cima de la montaña que domina el valle de Hinón hasta el extremo norte del valle de Refayín.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
Desde allí, el límite iba desde la cima de la montaña hasta el manantial de agua de Neftoa y hasta las ciudades del monte Efrón. Luego se doblaba hacia Balá (Quiriath-Yearín).
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
Luego el límite daba la vuelta al oeste de Baalá hasta el monte Seir y pasaba por la ladera norte del monte Yearín hasta la ciudad de Kesalón, bajaba a Bet Semes y seguía hasta Timná.
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
El límite seguía hasta la ladera norte de Ecrón y se doblaba hacia Siquerón, pasando por el monte Balá, hasta Jabneel y terminaba en el mar.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
El límite occidental era la costa del Gran Mar. Estos eran los límites alrededor de la tribu de Judá, por familias.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
El Señor le había ordenado a Josué que asignara algunas tierras en el territorio de Judá a Caleb, hijo de Jefone, y así se le dio la ciudad de Quiriat-arba, o Hebrón. (Arba era el padre de Anac).
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
Caleb expulsó a tres grupos familiares: Sesay, Ajimán y Talmai, descendientes de Anac.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
Desde allí fue a atacar a los habitantes de Debir (antes conocida como Quiriat-sefer).
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
Caleb anunció: “Al que ataque a Quiriat-sefer y lo capture, le daré a mi hija Acsa para que se case con él”.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
Otniel, hijo de Quenaz, hermano de Caleb, capturó la ciudad, por lo que Caleb le dio a su hija Acsa para que se casara.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
Cuando ella se acercó, él laconvenció para que le pidiera un campo a su padre. Y cuando ella se bajó del asno, Caleb le preguntó: “¿Qué quieres?”.
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
Ella respondió: “Por favor, dame una bendición. Ya que me has dado una tierra que es como el desierto, por favor, te pido que también me des manantiales de agua”. Entonces él le dio tanto el manantial superior como el inferior.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
Esta fue la tierra asignada a la tribu de Judá, por familias.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
Las ciudades para la tribu de Judá en el extremo sur, en la frontera con Edom: Cabzeel, Edar, Jagur,
22 Kina, Dimona, Adada,
Quiná, Dimoná, Adadá,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
Cedes, Jazor, Itnán,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Zif, Telén, Bealot,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
Jazor-jadatá, Queriot-Jezrón (o Jazor),
26 Amam, Shema, Molada,
Amán, Semá, Moladá,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
Jazar-Gadá, Hesmón, Bet-pelet,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
Jazar-súal, Beerseba, Biziotiá,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
Balá, Iyín, Esen,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
Eltolad, Quesil, Jormá,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
Siclag, Madmana, Sansaná,
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
Lebaot, Sijín, Ayín, y Rimón, es decir, veintinueve ciudades con sus aldeas.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
Las ciudades de las estribaciones occidentales: Estaol, Zora, Asena,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
Zanoa, Enganín, Tapúaj, Enam,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Jarmut, Adulán, Soco, Azeca,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
Sajarayin, Aditatin, Guederá, y Guederotayin, es decir, diez ciudades con sus aldeas.
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
También: Zenán, Jadasá, Migdal-gad,
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
Dileán, Mizpa, Joctel,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Laquis, Bocat, Eglón,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
Cabón, Lajmás, Quitlís,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Guederot, Bet-dagón, Noamá, y Maceda, es deicr, diez ciudades con sus aldeas.
42 Libna, Eter, Ashan,
Además: Libná, Éter, Asán,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
Jifta, Asena, Nezib,
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Queilá, Aczib y Maresá. Es decir, nueve ciudades con sus aldeas.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Ecrón, con sus ciudades y aldeas,
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
desde Ecrón hasta el mar las ciudades cercanas a Asdod y sus aldeas,
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Asdod y sus ciudades con sus aldeas, y Gaza con sus ciudades y aldeas, hasta el Wadi de Egipto, y a lo largo de la costa del mar.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
En la región de las colinas: Samir, Jatir, Soco,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
Daná, Quiriat Saná (o Debir),
50 Anab, Eshtemo, Anim,
Anab, Estemoa, Anín,
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
Gosén, Holón y Guiló. Es decir, once ciudades con sus aldeas.
52 Arab, Duma, Eshan,
También: Arab, Dumá, Esán,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
Yanún, Bet-tapúaj, Afecá,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Humtá, Quiriat-arba (o Hebrón), y Sior. Es decir, nueve ciudades con sus aldeas.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Además: Maón, Carmelo, Zif, Yutá,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
Jezrel, Jocdeán, Zanoa,
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Caín, Guibeá y Timná. Es deicr, diez ciudades con sus aldeas.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
También: Jaljul, Betsur, Guedor,
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Marat, Beth Anot y Eltecón. Es decir, seis ciudades con sus aldeas.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Además: Quiriat Baal (o Quiriat-Yearín) y Rabá. Es decir, dos ciudades con sus aldeas.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
En el desierto: Bet-arabá, Midín, Secacá,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Nibsán, la Ciudad de la Sal, y Engadi. Es decir, seis ciudades con sus aldea.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
Sin embargo, la tribu de Judá no pudo expulsar a los jebuseos, los habitantes de Jerusalén, por lo que los jebuseos viven entre la tribu de Judá en Jerusalén hasta el día de hoy.

< Yoshuwa 15 >