< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
El territorio que tocó en suerte a los hijos de la tribu de Judá, según sus familias, se extendía en el extremo meridional (del país), hasta el confín de Edom, hasta el desierto de Sin, al sur.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
Partía su frontera meridional, desde el extremo del Mar Salado, desde la lengua que mira hacia el sur;
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
se prolongaba hasta el lado meridional de la subida de Acrabim, pasaba a Sin, subía al sur de Cadesbarnea, corría hacia Hesrón, subía a Adar, y daba vuelta a Carcaá.
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
Luego pasaba a Asmón y se prolongaba hasta el torrente de Egipto, para terminar en el mar. “Esta será vuestra frontera meridional.”
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
La frontera oriental era el Mar Salado, hasta la desembocadura del Jordán. La frontera septentrional partía desde la lengua del mar, junto a la desembocadura del Jordán.
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
Subía la frontera hacia Bethoglá, y pasaba al norte de Betarabá; luego subía la frontera hasta la piedra de Bohan, hijo de Rubén.
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
Subía entonces la frontera a Dabir desde el valle de Acor, y por el norte torcía hacia Gálgala, que está frente a la subida de Adumim, al sur del torrente. La frontera pasaba hacia las aguas de En-Semes y terminaba en En- Rogel.
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
De allí subía la frontera por el valle de Ben Hinnom, por el lado meridional del jebuseo, que es Jerusalén. Luego subía la frontera a la cumbre del monte que está frente al valle de Hinnom, al occidente, y a la extremidad del valle de Refaím, al norte.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
Desde la cima del monte torcía la frontera a la fuente de las aguas de Neftoa y llegaba a las ciudades del monte de Efrón; luego la frontera seguía hacia Baalá, que es Kiryatyearim.
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
Desde Baalá se volvía la frontera al oeste, hacia el monte Seír, pasaba por la vertiente septentrional del monte Yearim que es Quesalón, bajaba a Betsemes y pasaba a Timná.
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
Después partía la frontera hacia la vertiente septentrional de Acarón, doblaba hacia Sicrón; pasaba por el monte de Baalá y salía a Jabneel para terminar en el mar.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
La frontera occidental era el Mar Grande con su costa. Estos fueron los términos de los hijos de Judá, a la redonda, según sus familias.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
Caleb, hijo de Jefone, recibió, por mandato de Yahvé dado a Josué, como porción en medio de los hijos de Judá, la ciudad de Arba, padre de Enac, que es Hebrón.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
Caleb arrojó de allí a los tres hijos de Enac: Sesai, Abimán y Talmai, hijos de Enac.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
De allí subió contra los habitantes de Dabir, que antiguamente se llamaba Kiryatséfer.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
Y dijo Caleb: “Al que derrotare a Kiryatséfer y la tomare, le daré por mujer a mi hija Acsá.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
La tomó Otoniel, hijo de Quenez, hermano de Caleb; y este le dio por mujer a su hija Acsá.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
Y aconteció que cuando ella se iba (con Otoniel), le instigó a que pidiese a su padre un campo; y como ella bajara del asno, le dijo Caleb: “¿Qué te pasa?”
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
Respondió ella: “Dame una bendición; ya que me has dado tierra de secano, dame también manantiales de agua.” Y él le dio manantiales en las regiones superiores y en las inferiores.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
Esta fue la heredad de la tribu de los hijos de Judá, según sus familias.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
Las ciudades de los hijos de Judá, en las extremidades meridionales de la tribu, hacia el territorio de Edom, eran: Cabseel, Eder, Jagur,
22 Kina, Dimona, Adada,
Ciná, Dimoná, Adadá,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
Cades, Hasor, Itnan,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Sif, Télem, Bealot,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
Hasor la nueva, Keriyothesrón, que es Hasor,
26 Amam, Shema, Molada,
Amam, Sema, Moladá,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
Hasargadá, Hesmón, Betfélet,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
Hazarsual, Bersabee, Bisiotiá,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
Baalá, Iyim, Esem,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
Eltolad, Quesil, Horma,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
Siclag, Madmaná, Sansaná,
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
Lebaot, Selhim, Ayin y Rimón; en total, veinte y nueve ciudades, con sus aldeas.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
En la Sefelá: Estaol, Zorá, Asna,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
Zanoa, Enganim, Tafua, Enam,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Jarmut, Adullam, Socó, Asecá,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
Saaraim, Aditaim, Gederá y Gederotaim: catorce ciudades con sus aldeas.
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
Senán, Hadasá, Migdalgad,
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
Dilán, Masfá, Jocteel,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Laquis, Boscat, Eglón,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
Cabón, Lahmam, Ketlís,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Gederot, Betdagón, Naama y Maquedá: diez y seis ciudades con sus aldeas.
42 Libna, Eter, Ashan,
Libná, Éter, Asan,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
Jeftá, Asna, Nesib,
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Queilá, Acsib y Maresá: nueve ciudades con sus aldeas.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Acarón con sus pueblos y sus aldeas;
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
desde Ecrón hacia el mar, todas las ciudades de la región de Azoto con sus aldeas;
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Azoto con sus pueblos y sus aldeas; Gaza con sus pueblos y sus aldeas, hasta el torrente de Egipto y el Mar Grande con su costa.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
En la montaña: Samir, Jatir, Socó,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
Daná, Kiryatsaná, que es Dabir;
50 Anab, Eshtemo, Anim,
Anab, Estemó, Anim,
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
Gosen, Holón y Giló: once ciudades con sus aldeas.
52 Arab, Duma, Eshan,
Arab, Dumá, Esán,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
Ianum, Bettafua, Afecá,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Humtá, Kiryatarbá, que es Hebrón, y Sior: nueve ciudades con sus aldeas.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maón, Carmel, Sif, Juta,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
Jesreel, Jocdeam, Sanoa,
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Caín, Gabaá y Timná: diez ciudades con sus aldeas.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul, Betsur, Gedor,
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Meará, Betanot y Eltecón; seis ciudades con sus aldeas.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Kiryatbaal, que es Kiryatyearim, y Rabbá: dos ciudades con sus aldeas.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
En el desierto: Betarabá, Midín, Secacá,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Nibsán, la ciudad de la Sal, y Engadí, seis ciudades con sus aldeas.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
Los hijos de Judá no pudieron expulsar a los jebuseos, que habitaban en Jerusalén, de manera que los jebuseos habitan con los hijos de Judá en Jerusalén hasta el día de hoy.

< Yoshuwa 15 >