< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
Und das Los des Stammes der Kinder Juda nach ihren Geschlechtern lag an der Grenze von Zin gegen Mittag, am südlichen Ende.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
Und ihre südliche Grenze beginnt am Ende des Salzmeeres, bei der Zunge, die mittagwärts reicht,
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
und zieht sich hinaus gegen Mittag zur Höhe von Akrabbim und hinüber gen Zin und wieder von Mittag gen Kadesch-Barnea hinauf und nach Hezron hin und gen Adar hinauf und wendet sich gegen Karka;
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
dann geht sie hinüber nach Azmon und hinaus an den Bach Ägyptens, so daß das Meer das Ende der Grenze bildet. Das sei eure südliche Grenze!
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
Aber die östliche Grenze ist das Salzmeer bis zur Mündung des Jordan. Die Grenze des nördlichen Teils aber beginnt bei der Zunge des Meeres an der Mündung des Jordan
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
und geht hinauf gen Beth-Hogla und zieht sich von Mitternacht gen Beth-Araba und kommt herauf zum Stein Bohan,
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
des Sohnes Rubens, und geht von dem Tal Achor hinauf gen Debir und wendet sich nördlich gegen Gilgal, welches der Anhöhe Adummim gegenüber liegt, das südlich an dem Bache liegt. Darnach geht sie zu dem Wasser En-Semes und kommt hinaus zum Brunnen Rogel,
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
geht darnach hinauf zum Tal des Sohnes Hinnoms, an der Seite der Jebusiter gegen Mittag, das ist Jerusalem; und sie kommt herauf zur Spitze des Berges, der westlich vor dem Tal Hinnom liegt und nördlich an das Ende des Tales Rephaim stößt.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
Darnach kommt sie von der Spitze desselben Berges zu der Quelle des Wassers Nephtoach und kommt heraus zu den Städten des Gebirges Ephron und neigt sich gen Baala, das ist Kirjat-Jearim.
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
Und die Grenze wendet sich herum von Baala gegen Abend zum Gebirge Seir und geht hinüber nach dem nördlichen Bergrücken Jearim, das ist Kesalon, und kommt herab gen Beth-Semes und geht nach Timna;
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
sodann läuft die Grenze weiter nördlich bis zum Bergrücken von Ekron und zieht sich gen Sikron und geht über den Berg Baala und kommt heraus gen Jabneel; also daß das Meer das Ende dieser Grenze bildet.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
Die Grenze aber gegen Abend ist das große Meer und sein Gestade. Das ist die Grenze der Kinder Juda, nach ihren Geschlechtern, ringsum.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
Aber Kaleb, dem Sohn Jephunnes, gab er sein Teil unter den Kindern Juda nach dem Befehl des HERRN an Josua, nämlich die Stadt Arba, des Vaters Enaks, das ist Hebron.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
Und Kaleb vertrieb von dannen die drei Söhne Enaks, Sesai, Achiman und Talmai, die Enakskinder,
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
und zog von dannen hinauf zu den Einwohnern von Debir. Debir aber hieß vor Zeiten Kirjat-Sepher.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
Und Kaleb sprach: Wer Kirjat-Sepher schlägt und erobert, dem will ich meine Tochter Achsa zum Eheweib geben!
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
Da gewann sie Otniel, der Sohn Kenas, des Bruders Kalebs; und er gab ihm seine Tochter Achsa zum Eheweib.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
Und es begab sich, als sie einzog, trieb sie ihn an, von ihrem Vater einen Acker zu fordern. Und sie sprang vom Esel. Da sprach Kaleb zu ihr:
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
Was hast du? Sie sprach: Gib mir einen Segen, denn du hast mir ein dürres Land gegeben; gib mir auch Wasserquellen! Da gab er ihr Wasserquellen, die obern und die untern.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
Das ist das Erbteil des Stammes der Kinder Juda nach ihren Geschlechtern.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
Und die äußersten Städte des Stammes der Kinder Juda, gegen die Grenze der Edomiter im Süden, waren diese: Kabzeel,
22 Kina, Dimona, Adada,
Eder, Jagur, Kina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
Kedesch, Hazor, Jitnan, Siph, Telem,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Bealot, Hazor-Hadatta, Keriot-Hezron,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
welches Hazor ist,
26 Amam, Shema, Molada,
Amam, Sema, Molada,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
Hazar-Gadda, Hesmon, Beth-Pelet,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
Hazar-Schual, Beer-Seba, Bisjot-Ja,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
Baala, Jjim, Ezem, Eltolad, Kesil,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
Horma, Ziklag, Madmanna, Sansanna,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
Lebaot, Silhim, Ain und Rimmon.
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
Das sind neunundzwanzig Städte und ihre Dörfer.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
In den Tälern aber waren Estaol,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
Zorea, Asna, Sanoach, En-Gannim,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Tappuach, Enam, Jarmut,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
Adullam, Socho, Aseka, Saaraim, Aditaim, Gereda, Gederotaim;
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
das sind vierzehn Städte und ihre Dörfer.
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
Zenan, Hadasa, Migdal-Gad, Dilean,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Mizpe, Jokteel, Lachis, Bozkat, Eglon,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
Kabbon, Lachmas, Kitlis, Gederot,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Beth-Dagon, Naama, Makkeda. Das sind sechzehn Städte und ihre Dörfer.
42 Libna, Eter, Ashan,
Libna, Eter, Asan, Jiphtach, Asna, Nezib,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
Kegila, Achsib, Maresa.
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Das sind neun Städte und ihre Dörfer.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Ekron, mit seinen Dörfern und Höfen.
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
Von Ekron und bis an das Meer alles, was an Asdod grenzt und ihre Dörfer:
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Asdod mit seinen Dörfern und Höfen, Gaza mit seinen Höfen und Dörfern, bis an den Bach Ägyptens, und das große Meer ist seine Grenze.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
Auf dem Gebirge aber waren Samir, Jattir, Socho,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
Danna, Kirjat-Sanna, welches Debir ist,
50 Anab, Eshtemo, Anim,
Anab, Estemo, Anim, Gosen, Holon, Gilo.
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
Das sind elf Städte und ihre Dörfer.
52 Arab, Duma, Eshan,
Arab, Duma, Esean,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
Janum, Beth-Tappuach, Apheka, Humta,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Kirjat-Arba, das ist Hebron, Zior. Das sind neun Städte und ihre Dörfer.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maon, Karmel, Siph, Juta, Jesreel,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
Jokdeam, Sanoach, Kain, Gibea, Timna.
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Das sind zehn Städte und ihre Dörfer.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul, Beth-Zur, Gedor, Maarat, Beth-Anot und Eltekon.
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Das sind sechs Städte und ihre Dörfer.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Kirjat-Baal, das ist Kirjat-Jearim, und Rabba. Das sind zwei Städte und ihre Dörfer.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
In der Wüste aber waren Beth-Araba, Middin,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Sechacha, Nibsan und die Salzstadt und Engedi. Das sind sechs Städte und ihre Dörfer.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
Die Kinder Juda aber konnten die Jebusiter, welche zu Jerusalem wohnten, nicht vertreiben. Also wohnten die Jebusiter mit den Kindern Juda zu Jerusalem bis auf diesen Tag.

< Yoshuwa 15 >