< Yoshuwa 15 >
1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
And it was the lot of [the] tribe of [the] descendants of Judah to clans their to [the] border of Edom [the] wilderness of Zin [the] south towards from [the] end of [the] south.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
And it was to them border of [the] south from [the] end of [the] Sea of Salt from the bay which faces [the] south towards.
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
And it goes out to from [the] south of [the] ascent of scorpions and it passes on Zin towards and it goes up from [the] south of Kadesh Barnea and it passes on Hezron and it goes up Addar towards and it turns Karka towards.
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
And it passes on Azmon towards and it goes out [the] wadi of Egypt (and they are *Q(K)*) ([the] extremities of *LAH(b)*) the territory west-ward this it will be of you border of [the] south.
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
And [the] border east-ward [is] [the] Sea of Salt to [the] end of the Jordan and [the] border of [the] side of north-ward [is] from [the] bay of the sea from [the] end of the Jordan.
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
And it goes up the border Beth Hoglah and it passes on from [the] north of Beth Arabah and it goes up the border [the] stone of Bohan [the] son of Reuben.
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
And it goes up the border - Debir towards from [the] valley of Achor and north-ward [it is] turning to Gilgal which [is] opposite to [the] ascent of Adummim which [is] from [the] south of the wadi and it passes on the border to [the] waters of En Shemesh and they are extremities its to En Rogel.
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
And it goes up the border [the] valley of Ben Hinnom to [the] slope of the Jebusite[s] from [the] south that [is] Jerusalem and it goes up the border to [the] top of the mountain which [is] on [the] face of [the] valley of [Ben] Hinnom west-ward which [is] at [the] end of [the] valley of [the] Rephaites north-ward.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
And it turns the border from [the] top of the mountain to [the] spring of [the] waters of Nephtoah and it goes out to [the] cities of [the] mountain of Ephron and it turns the border Baalah that [is] Kiriath Jearim.
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
And it turns the border from Baalah west-ward to [the] mountain of Seir and it passes on to [the] slope of [the] mountain of Jearim from north-ward that [is] Kesalon and it goes down Beth Shemesh and it passes on Timnah.
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
And it goes out the border to [the] slope of Ekron north-ward and it turns the border Shikkeron towards and it passes on [the] mountain of Baalah and it goes out Jabneel and they are [the] extremities of the territory west-ward.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
And [the] border of [the] west [is] the sea towards great and territory this [is] [the] border of [the] descendants of Judah around to clans their.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
And to Caleb [the] son of Jephunneh someone gave a portion in among [the] descendants of Judah to [the] mouth of Yahweh to Joshua Kiriath Arba [the] father of Anak that [is] Hebron.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
And he dispossessed from there Caleb three [the] sons of Anak Sheshai and Ahiman and Talmai those born of Anak.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
And he went up from there against [the] inhabitants of Debir and [the] name of Debir before [was] Kiriath Sepher.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
And he said Caleb [the one] who he will strike Kiriath Sepher and he will capture it and I will give to him Achsah daughter my to a wife.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
And he captured it Othniel [the] son of Kenaz [the] brother of Caleb and he gave to him Achsah daughter his to a wife.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
And it was when came she and she incited him to ask from with father her a field and she went down from on the donkey and he said to her Caleb what? [is] to you.
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
And she said give! to me a blessing for [the] land of the Negev you have given to me and you will give to me springs of water and he gave to her springs upper and springs lower.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
This [was] [the] inheritance of [the] tribe of [the] descendants of Judah to clans their.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
And they were the cities from [the] end of [the] tribe of [the] descendants of Judah to [the] border of Edom in the south Kabzeel and Eder and Jagur.
And Kinah and Dimonah and Adadah.
And Kedesh and Hazor and Ithnan.
Ziph and Telem and Bealoth.
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
And Hazor - Hadattah and Kerioth Hezron that [is] Hazor.
Amam and Shema and Moladah.
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
And Hazar Gaddah and Heshmon and Beth Pelet.
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
And Hazar Shual and Beer Sheba and Biziothiah.
30 Eltolad, Kesil, Horma,
And Eltolad and Kesil and Hormah.
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
And Ziklag and Madmannah and Sansannah.
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
And Lebaoth and Shilhim and Ain and Rimmon all [the] cities [were] twenty and nine and villages their.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
In the Shephelah Eshtaol and Zorah and Ashnah.
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
And Zanoah and En Gannim Tappuah and Enam.
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Jarmuth and Adullam Socoh and Azekah.
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
And Shaaraim and Adithaim and Gederah and Gederothaim cities four-teen and villages their.
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
Zenan and Hadashah and Migdal Gad.
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
And Dilean and Mizpah and Joktheel.
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Lachish and Bozkath and Eglon.
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
And Cabbon and Lahmas and Kitlish.
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
And Gederoth Beth Dagon and Naamah and Makkedah cities six-teen and villages their.
Libnah and Ether and Ashan.
And Iphtah and Ashnah and Nezib.
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
And Keilah and Aczib and Mareshah cities nine and villages their.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Ekron and daughters its and villages its.
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
From Ekron and west-ward all that [is] on [the] hand of Ashdod and villages their.
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Ashdod daughters its and villages its Gaza daughters its and villages its to [the] wadi of Egypt and the sea (great *Q(K)*) and territory.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
And in the hill country Shamir and Jattir and Socoh.
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
And Dannah and Kiriath Sannah that [is] Debir.
And Anab and Eshtemoh and Anim.
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
And Goshen and Holon and Giloh cities one [plus] ten and villages their.
Arab and Rumah and Eshan.
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
(And Janum *Q(K)*) and Beth Tappuah and Aphekah.
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
And Humtah and Kiriath Arba that [is] Hebron and Zior cities nine and villages their.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maon - Carmel and Ziph and Juttah.
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
And Jezreel and Jokdeam and Zanoah.
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Kain Gibeah and Timnah cities ten and villages their.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul Beth Zur and Gedor.
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
And Maarath and Beth Anoth and Eltekon cities six and villages their.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Kiriath Baal that [is] Kiriath Jearim and Rabbah cities two and villages their.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
In the wilderness Beth Arabah Middin and Secacah.
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
And Nibshan and [the] city of Salt and En Gedi cities six and villages their.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
And the Jebusite[s] [the] inhabitants of Jerusalem not (they were able *Q(K)*) [the] descendants of Judah to dispossess them and he has dwelt the Jebusite[s] with [the] descendants of Judah in Jerusalem until the day this.