< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
This then was the lot of the tribe of the children of Judah by their families; even to the border of Edom the wilderness of Zin southward was the uttermost part of the south coast.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
And their south border was from the shore of the salt sea, from the bay that looks southward:
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
And it went out to the south side to Maalehacrabbim, and passed along to Zin, and ascended up on the south side to Kadeshbarnea, and passed along to Hezron, and went up to Adar, and fetched a compass to Karkaa:
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
From there it passed toward Azmon, and went out to the river of Egypt; and the goings out of that coast were at the sea: this shall be your south coast.
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
And the east border was the salt sea, even to the end of Jordan. And their border in the north quarter was from the bay of the sea at the uttermost part of Jordan:
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
And the border went up to Bethhogla, and passed along by the north of Betharabah; and the border went up to the stone of Bohan the son of Reuben:
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
And the border went up toward Debir from the valley of Achor, and so northward, looking toward Gilgal, that is before the going up to Adummim, which is on the south side of the river: and the border passed toward the waters of Enshemesh, and the goings out thereof were at Enrogel:
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
And the border went up by the valley of the son of Hinnom to the south side of the Jebusite; the same is Jerusalem: and the border went up to the top of the mountain that lies before the valley of Hinnom westward, which is at the end of the valley of the giants northward:
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
And the border was drawn from the top of the hill to the fountain of the water of Nephtoah, and went out to the cities of mount Ephron; and the border was drawn to Baalah, which is Kirjathjearim:
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
And the border compassed from Baalah westward to mount Seir, and passed along to the side of mount Jearim, which is Chesalon, on the north side, and went down to Bethshemesh, and passed on to Timnah:
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
And the border went out to the side of Ekron northward: and the border was drawn to Shicron, and passed along to mount Baalah, and went out to Jabneel; and the goings out of the border were at the sea.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
And the west border was to the great sea, and the coast thereof. This is the coast of the children of Judah round about according to their families.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
And to Caleb the son of Jephunneh he gave a part among the children of Judah, according to the commandment of the LORD to Joshua, even the city of Arba the father of Anak, which city is Hebron.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
And Caleb drove there the three sons of Anak, Sheshai, and Ahiman, and Talmai, the children of Anak.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
And he went up there to the inhabitants of Debir: and the name of Debir before was Kirjathsepher.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
And Caleb said, He that smites Kirjathsepher, and takes it, to him will I give Achsah my daughter to wife.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
And Othniel the son of Kenaz, the brother of Caleb, took it: and he gave him Achsah his daughter to wife.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
And it came to pass, as she came to him, that she moved him to ask of her father a field: and she lighted off her ass; and Caleb said to her, What would you?
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
Who answered, Give me a blessing; for you have given me a south land; give me also springs of water. And he gave her the upper springs, and the nether springs.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the children of Judah according to their families.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
And the uttermost cities of the tribe of the children of Judah toward the coast of Edom southward were Kabzeel, and Eder, and Jagur,
22 Kina, Dimona, Adada,
And Kinah, and Dimonah, and Adadah,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
And Kedesh, and Hazor, and Ithnan,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Ziph, and Telem, and Bealoth,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
And Hazor, Hadattah, and Kerioth, and Hezron, which is Hazor,
26 Amam, Shema, Molada,
Amam, and Shema, and Moladah,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
And Hazargaddah, and Heshmon, and Bethpalet,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
And Hazarshual, and Beersheba, and Bizjothjah,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
Baalah, and Iim, and Azem,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
And Eltolad, and Chesil, and Hormah,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
And Ziklag, and Madmannah, and Sansannah,
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
And Lebaoth, and Shilhim, and Ain, and Rimmon: all the cities are twenty and nine, with their villages:
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
And in the valley, Eshtaol, and Zoreah, and Ashnah,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
And Zanoah, and Engannim, Tappuah, and Enam,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Jarmuth, and Adullam, Socoh, and Azekah,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
And Sharaim, and Adithaim, and Gederah, and Gederothaim; fourteen cities with their villages:
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
Zenan, and Hadashah, and Migdalgad,
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
And Dilean, and Mizpeh, and Joktheel,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Lachish, and Bozkath, and Eglon,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
And Cabbon, and Lahmam, and Kithlish,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
And Gederoth, Bethdagon, and Naamah, and Makkedah; sixteen cities with their villages:
42 Libna, Eter, Ashan,
Libnah, and Ether, and Ashan,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
And Jiphtah, and Ashnah, and Nezib,
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
And Keilah, and Achzib, and Mareshah; nine cities with their villages:
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Ekron, with her towns and her villages:
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
From Ekron even to the sea, all that lay near Ashdod, with their villages:
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Ashdod with her towns and her villages, Gaza with her towns and her villages, to the river of Egypt, and the great sea, and the border thereof:
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
And in the mountains, Shamir, and Jattir, and Socoh,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
And Dannah, and Kirjathsannah, which is Debir,
50 Anab, Eshtemo, Anim,
And Anab, and Eshtemoh, and Anim,
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
And Goshen, and Holon, and Giloh; eleven cities with their villages:
52 Arab, Duma, Eshan,
Arab, and Dumah, and Eshean,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
And Janum, and Bethtappuah, and Aphekah,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
And Humtah, and Kirjatharba, which is Hebron, and Zior; nine cities with their villages:
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maon, Carmel, and Ziph, and Juttah,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
And Jezreel, and Jokdeam, and Zanoah,
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Cain, Gibeah, and Timnah; ten cities with their villages:
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul, Bethzur, and Gedor,
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
And Maarath, and Bethanoth, and Eltekon; six cities with their villages:
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Kirjathbaal, which is Kirjathjearim, and Rabbah; two cities with their villages:
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
In the wilderness, Betharabah, Middin, and Secacah,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
And Nibshan, and the city of Salt, and Engedi; six cities with their villages.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
As for the Jebusites the inhabitants of Jerusalem, the children of Judah could not drive them out; but the Jebusites dwell with the children of Judah at Jerusalem to this day.

< Yoshuwa 15 >