< Yoshuwa 14 >

1 Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
To so dežele, ki so jih Izraelovi otroci podedovali v kánaanski deželi, ki so jim jo duhovnik Eleazar, Nunov sin Józue in poglavarji očetov rodov Izraelovih otrok razdelili v dediščino.
2 Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Njihova dediščina je bila po žrebu, kakor je Gospod zapovedal po Mojzesovi roki, za devet rodov in za polovico rodu.
3 Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
Kajti Mojzes je na drugi strani Jordana dal dediščino dvema rodovoma in polovici rodu, toda Lévijevcem med njimi ni dal nobene dediščine.
4 gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
Kajti od Jožefovih otrok sta bila dva rodova, Manáse in Efrájim. Zato v deželi niso dali nobenega deleža Lévijevcem, razen mest, da prebivajo v njih, z njihovimi predmestji za njihovo živino in za njihovo imetje.
5 Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Kakor je Gospod zapovedal Mojzesu, tako so Izraelovi otroci storili in razdelili so deželo.
6 Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
Potem so Judovi otroci prišli k Józuetu v Gilgál in Jefunéjev sin Kaléb, Kenázovec, mu je rekel: »Ti poznaš stvar, ki jo je Gospod rekel Božjemu možu Mojzesu glede mene in tebe v Kadeš Barnéi.
7 Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
Štirideset let mi je bilo, ko me je Gospodov služabnik Mojzes poslal iz Kadeš Barnée, da ogledam deželo in ponovno sem mu prinesel besedo, kakor je bila ta v mojem srcu.
8 amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
Kljub temu so moji bratje, ki so z menoj odšli gor, ljudstvu stopili srce, toda jaz sem v celoti sledil Gospodu, svojemu Bogu.
9 Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
Mojzes je na ta dan prisegel, rekoč: ›Zagotovo bo dežela, ki si jo pomendral s svojimi stopali, tvoja dediščina in tvojih otrok na veke, ker si v celoti sledil Gospodu, mojemu Bogu.‹
10 “Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
Sedaj, glej, Gospod me je obdržal živega, kakor je rekel, teh petinštirideset let, celo odkar je Gospod spregovoril to besedo Mojzesu, medtem ko so Izraelovi otroci tavali po divjini. Sedaj glej, jaz sem danes star petinosemdeset let.
11 Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
Še danes sem tako močan, kakor sem bil na dan, ko me je poslal Mojzes. Kakršna je bila moja moč takrat, celo takšna je moja moč za vojno zdaj, tako za odhajanje kakor za prihajanje.
12 Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
Zdaj mi torej daj to goro, o kateri je Gospod govoril na tisti dan, kajti na tisti dan si slišal kako so bili tam Anákovci in da so bila mesta velika in ograjena. Če bo tako, da bo Gospod z menoj, potem jih bom zmožen pognati ven, kakor je rekel Gospod.«
13 Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
Józue ga je blagoslovil in Jefunéjevemu sinu Kalébu v dediščino izročil Hebrón.
14 Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
Hebrón je torej postal dediščina Jefunéjevega sina Kaléba, Kenázovca, do tega dne, zato ker je v celoti sledil Gospodu, Izraelovemu Bogu.
15 (Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.
Ime Hebróna je bilo prej Kirját Arba; ta Arbá je bil velik mož med Anákovci. In dežela je imela počitek pred vojno.

< Yoshuwa 14 >