< Yoshuwa 14 >
1 Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
Und dies ist, was die Söhne Israels im Lande Kanaan als Erbe erhielten, das ihnen zum Erbe verteilten Eleasar, der Priester, und Joschua, der Sohn Nuns, und die Häupter der Väter der Stämme, der Söhne Israels.
2 Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Durch das Los, wie Jehovah durch Mose geboten hatte, verteilten sie das Erbe den neun Stämmen und dem halben Stamm.
3 Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
Denn Mose hatte den zwei Stämmen und dem halben Stamm das Erbe jenseits des Jordans gegeben, und den Leviten gab er kein Erbe in ihrer Mitte.
4 gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
Denn die Söhne Josephs wurden zwei Stämme: Menascheh und Ephraim; und den Leviten gaben sie keinen Teil im Lande, sondern Städte zum Wohnen und deren Weichbilde für ihre Viehherden und ihren Besitz.
5 Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Wie Jehovah Mose geboten hatte, so taten die Söhne Israels und verteilten das Land.
6 Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
Und die Söhne Judahs traten herzu zu Joschua in Gilgal; und Kaleb, der Sohn Jephunnehs, der Kenissite, sprach zu ihm: Du weißt das Wort, das Jehovah zu Mose, dem Manne Gottes, in Kadesch Barnea meinetwegen und deinetwegen geredet hat.
7 Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
Vierzig Jahre war ich alt, als Mose der Knecht Jehovahs, mich aus Kadesch Barnea sandte, das Land auszukundschaften, und ich brachte ihm Nachricht zurück, wie es in meinem Herzen war.
8 amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
Aber meine Brüder, die mit mir hinaufgezogen waren, machten das Herz des Volkes zerschmelzen; ich aber folgte Jehovah, meinem Gotte, völlig.
9 Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
Und Mose schwur selbigen Tages und sprach: Fürwahr, das Land, das dein Fuß betreten hat, soll dir und deinen Söhnen zum Erbe sein ewiglich; denn du folgtest Jehovah, meinem Gotte, völlig.
10 “Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
Und nun siehe, Jehovah hat mich am Leben erhalten, wie Er geredet hat, diese fünfundvierzig Jahre, seit Jehovah dies Wort geredet hat zu Mose, da Israel in der Wüste zog, und nun siehe, ich bin diesen Tag fünfundachtzig Jahre alt.
11 Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
Noch bin ich diesen Tag so stark, wie am Tage, da Mose mich sandte; wie meine Kraft war damals, so ist meine Kraft jetzt, zum Streit, zum Ausgang und zum Eingang.
12 Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
Und nun, gib mir diesen Berg, davon Jehovah an selbigem Tag geredet hat. Denn du hast an demselben Tage gehört, daß Enakim dort sind, und große, feste Städte. Vielleicht ist Jehovah mit mir, daß ich sie austreibe, wie Jehovah geredet hat.
13 Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
Und Joschua segnete ihn und gab Chebron dem Kaleb, dem Sohne Jephunnehs, zum Erbe.
14 Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
Deshalb ward Chebron dem Kaleb, dem Sohne Jephunnehs, dem Kenissiten zum Erbe bis auf diesen Tag, darum, daß er Jehovah, dem Gotte Israels, völlig gefolgt.
15 (Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.
Und der Name Chebron war vordem Kirjath Arbah, eines Menschen, der groß war unter den Enakim; und das Land rastete vom Krieg.