< Yoshuwa 14 >
1 Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
Ce sont ici [les terres] que les enfants d'Israël eurent pour héritage au pays de Canaan, qu'Eléazar le Sacrificateur, et Josué, fils de Nun, et les chefs des pères des Tribus des enfants d'Israël leur partagèrent en héritage.
2 Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Selon le sort de leur héritage, comme l'Eternel l'avait commandé par le moyen de Moïse, [savoir] à neuf Tribus, et à la moitié d'une Tribu.
3 Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
Car Moïse avait donné un héritage à deux Tribus, et à la moitié d'une Tribu au delà du Jourdain, mais il n'avait point donné d'héritage parmi eux aux Lévites.
4 gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
Parce que les enfants de Joseph, [savoir], Manassé et Ephraïm, faisaient deux Tribus; et on ne donna point de part aux Lévites dans le pays, excepté les villes pour y habiter avec leurs fauxbourgs pour leurs troupeaux, et pour [le reste de] leur bien.
5 Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Les enfants d'Israël firent comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse, et ils partagèrent la terre.
6 Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
Or les enfants de Juda vinrent à Josué en Guilgal; et Caleb fils de Jéphunné Kénizien, lui dit: Tu sais la parole que l'Eternel a dite de moi, et de toi, à Moïse homme de Dieu, en Kadès-barné.
7 Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
J'étais âgé de quarante ans quand Moïse serviteur de l'Eternel m'envoya de Kadès-barné pour reconnaître le pays, et je lui rapportai la chose comme elle était en mon cœur.
8 amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
Et mes frères qui étaient montés avec moi, faisaient fondre le cœur du peuple; mais je persévérai à suivre l'Eternel mon Dieu.
9 Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
Et Moïse jura en ce jour-là disant: Si la terre sur laquelle ton pied a marché n'est à toi en héritage, et à tes enfants pour jamais; parce que tu as persévéré à suivre l'Eternel mon Dieu.
10 “Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
Or maintenant voici, l'Eternel m'a fait vivre selon qu'il en avait parlé; il y a déjà quarante-cinq ans que l'Eternel prononça cette parole à Moïse, lorsque Israël marchait par le désert, et maintenant voici, je suis aujourd'hui âgé de quatre-vingt et cinq ans.
11 Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
Et [je] suis encore aujourd'hui aussi fort que j'étais le jour que Moïse m'envoya, et j'ai maintenant la même force que j'avais alors pour le combat, et pour aller et venir.
12 Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
Maintenant donc donne-moi cette montagne, de laquelle l'Eternel parla en ce jour-là; car tu entendis en ce jour-là que les Hanakins y habitent, et qu'il y a de grandes villes fortes; peut-être que l'Eternel sera avec moi, et je les déposséderai, comme l'Eternel en a parlé.
13 Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
Josué donc le bénit, et donna Hébron en héritage à Caleb, fils de Jéphunné.
14 Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
C'est pourquoi Hébron fut à Caleb, fils de Jéphunné Kénizien, en héritage jusqu'à ce jour, parce qu'il avait persévéré à suivre l'Eternel, le Dieu d'Israël.
15 (Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.
Or le nom d'Hébron était auparavant Kirjath-Arbah, et [Arbah] avait été un fort grand homme entre les Hanakins. Et le pays fut tranquille sans avoir guerre.