< Yoshuwa 13 >

1 Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
Era, porém, Josué já velho, entrado em dias; e disse-lhe o Senhor: Já estás velho, entrado em dias; e ainda muitíssima terra ficou para possuir.
2 “Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
A terra que fica de resto é esta: todos os termos dos philisteus, e toda a Gesuri;
3 Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
Desde Sihor, que está defronte do Egito, até ao termo de Ekron para o norte, que se conta ser dos cananeus: cinco príncipes dos philisteus, o gazeu, e o asdodeu, o ascalonita, o getheu, e o ekroneu, e os aveus;
4 Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
Desde o sul, toda a terra dos cananeus, e Meara, que é dos sidôneos; até Aphek: até ao termo dos amorreus;
5 da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
Como também a terra dos gibleus, e todo o líbano para o nascente do sol, desde Baal-gad, ao pé do monte Hermon, até à entrada de Hamath;
6 “Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
Todos os que habitam nas montanhas desde o líbano até Misrephoth-main, todos os sidôneos; eu os lançarei de diante dos filhos de Israel: tão somente faze que a terra caia a Israel em sorte por herança, como já to tenho mandado.
7 ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
Reparte pois agora esta terra por herança às nove tribos e à meia tribo de Manasseh;
8 Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
Com quem os rubenitas e os gaditas já receberam a sua herança; a qual lhes deu Moisés de além do Jordão para o oriente; como já lhes tinha dado Moisés, servo do Senhor,
9 Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
Desde Aroer, que está à borda do ribeiro de Arnon, e a cidade que está no meio do vale, e toda a campina de Medeba até Dibon;
10 da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
E todas as cidades de Sehon, rei dos amorreus, que reinou em Hesbon, até ao termo dos filhos de Ammon;
11 Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
E Gilead, e o termo dos gesureus, e dos maacateus, e todo o monte Hermon, e toda a Basan até Salcha:
12 wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
Todo o reino de Og em Basan, que reinou em Astaroth e em Edrei; este ficou do resto dos gigantes que Moisés feriu e expeliu.
13 Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
Porém os filhos de Israel não expeliram os gesureus, nem os maacateus; antes Gesur e Maacath habitaram no meio de Israel até ao dia de hoje.
14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Tão somente à tribo de Levi não deu herança: os sacrifícios queimados do Senhor Deus de Israel são a sua herança, como já lhe tinha dito.
15 Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
Assim Moisés deu à tribo dos filhos de Ruben, conforme as suas famílias.
16 Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
E foi o seu termo desde Aroer, que está à borda do ribeiro de Arnon, e a cidade que está no meio do vale, e toda a campina até Medeba;
17 zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
Hesbon e todas as suas cidades, que estão na campina: Dibon, e Bamoth-baal, e Beth-baal-meon;
18 Yahza, Kedemot, Mefa’at,
E Jahsa, e Kedemoth, e Mephaat;
19 Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
E Kiriathaim, e Sibma, e Zereth, e Hassahar, no monte do vale;
20 Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
E Beth-peor, e Asdoth-pisga, e Beth-jesimoth;
21 dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
E todas as cidades da campina, e todo o reino de Sehon, rei dos amorreus, que reinou em Hesbon, a quem Moisés feriu, como também aos príncipes de Midian, Evi, e Rekem, e Sur, e Hur, e Reba, príncipes de Sehon, moradores da terra.
22 Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
Também os filhos de Israel mataram à espada a Balaão, filho de Beor, o adivinho, como os mais que por eles foram mortos.
23 Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
E foi o termo dos filhos de Ruben o Jordão e o seu termo; esta é a herança dos filhos de Ruben, segundo as suas famílias, as cidades, e as suas aldeias.
24 Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
E deu Moisés à tribo de Gad, aos filhos de Gad, segundo as suas famílias.
25 Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
E foi o seu termo Jaezer, e todas as cidades de Gilead, e metade da terra dos filhos de Ammon, até Aroer, que está defronte de Rabba;
26 da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
E desde Hesbon até Ramath-mispe, e Bethonim: e desde Mahanaim até ao termo de Debir;
27 kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
E no vale Beth-aram, e Beth-nimra, e Succoth, e Saphon, que ficara do resto do reino do rei de Sehon em Hesbon, o Jordão e o seu termo, até à extremidade do mar de Cinnereth de além do Jordão para o oriente.
28 Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
Esta é a herança dos filhos de Gad, segundo as suas famílias, as cidades e as suas aldeias.
29 Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
Deu também Moisés herança à meia tribo de Manasseh, que ficou à meia tribo dos filhos de Manasseh, segundo as suas famílias,
30 Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
De maneira que o seu termo foi desde Mahanaim, todo o Basan, todo o reino de Og, rei de Basan, e todas as aldeias de Jair, que estão em Basan, sessenta cidades,
31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
E metade de Gilead, e Astaroth, e Edrei, cidades do reino de Og, em Basan, aos filhos de Machir, filho de Manasseh, a saber, à metade dos filhos de Machir, segundo as suas famílias.
32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
Isto é o que Moisés repartiu em herança nas campinas de Moab, de além do Jordão de Jericó para o oriente.
33 Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.
Porém à tribo de Levi Moisés não deu herança: o Senhor Deus de Israel é a sua herança, como já lhe tinha dito.

< Yoshuwa 13 >