< Yoshuwa 13 >

1 Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
Josué était vieux et d’un âge fort avancé, et le Seigneur lui dit: Tu es vieux, et même très avancé en âge, et une terre très étendue est restée, qui n’a pas été encore divisée par le sort:
2 “Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
Savoir, toute la Galilée, la terre des Philistins et toute celle de Gessuri,
3 Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
Depuis le fleuve fangeux qui arrose l’Egypte jusqu’aux confins d’Accaron, contre l’aquilon; la terre de Chanaan qui est partagée entre les cinq princes des Philistins, celui de Gaza, celui d’Azot, celui d’Ascalon, celui de Geth et celui d’Accaron.
4 Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
Mais au midi sont les Hévéens, toute la terre de Chanaan, Maara des Sidoniens, jusqu’à Aphéca et jusqu’aux frontières des Amorrhéens,
5 da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
Et jusqu’aux pays qui leur sont voisins; de plus, la contrée du Liban contre l’orient, depuis Baalgad, au-dessous de la montagne d’Hermon, jusqu’à ce qu’on entre à Emath;
6 “Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
La contrée de tous ceux qui habitent sur la montagne, depuis le Liban jusqu’aux eaux de Maséréphoth, et tous les Sidoniens. Je suis celui qui les exterminerai de la face des enfants d’Israël. Que cela entre donc dans la part de l’héritage d’Israël, comme je t’ai ordonné.
7 ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
Et maintenant partage la terre en possession aux neuf tribus, et à la demi-tribu de Manassé,
8 Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
Avec laquelle Ruben et Gad possédèrent déjà la terre que leur a livrée Moïse, serviteur du Seigneur, au-delà des courants du Jourdain, du côté oriental,
9 Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
Depuis Aroer, qui est située sur la rive du torrent d’Arnon, et au milieu de la vallée; de plus, toute la campagne de Médaba, jusqu’à Dibon;
10 da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
Et toutes les villes de Séhon, roi de l’Amorrhéen, lequel a régné à Hésébon, jusqu’aux frontières des enfants d’Ammon:
11 Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
Galaad, les confins de Gessuri et de Machati; toute la montagne d’Hermon, et tout le Basan, jusqu’à Salécha,
12 wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
Tout le royaume d’Og en Basan, lequel a régné à Astaroth et à Edraï, et qui était des restes des Raphaïm; et Moïse les battit et les détruisit.
13 Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
Cependant les enfants d’Israël ne voulurent pas exterminer ceux de Gessuri et de Machati; aussi ont-ils habité au milieu d’Israël jusqu’au présent jour.
14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Mais à la tribu de Lévi. Moïse ne donna point de possession, parce que les sacrifices et les victimes du Seigneur Dieu d’Israël sont son héritage, comme lui a dit le Seigneur.
15 Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
Moïse donna donc des possessions à la tribu des enfants de Ruben, selon sa parenté.
16 Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
Et sa limite fut depuis Aroer, qui est située sur la rive du torrent d’Arnon, et au milieu de la vallée du même torrent, toute la plaine qui conduit à Médaba,
17 zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
Hésébon, et tous leurs villages qui sont dans la campagne; Dibon aussi, Bamothbaal, la ville de Baalméon,
18 Yahza, Kedemot, Mefa’at,
Jassa, Cédimoth, Méphaath,
19 Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
Cariathaïm, Sabama, Sarathasar sur la montagne de la vallée,
20 Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
Bethphogor et Asédoth, Phasga et Bethiésimoth,
21 dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
Et toutes les villes de la plaine, tous les royaumes de Séhon, roi de l’Amorrhéen, qui régna à Hésébon, que Moïse battit avec les princes de Madian, Hévi, Résem, Sur, Hur et Rébé, chefs de Séhon, habitants de cette terre.
22 Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
Et les enfants d’Israël firent mourir par le glaive Balaam le devin, fils de Béor, avec tous les autres qui furent tués,
23 Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
Et le Jourdain devint la limite des enfants de Ruben. C’est là la possession des villes et des villages des Rubénites, selon leur parenté.
24 Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
Moïse donna aussi à la tribu de Gad et a ses enfants, selon leur parenté, une possession dont voici la division:
25 Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
Sa limite fut Jaser, toutes les villes de Galaad, et la moitié de la terre des enfants d’Ammon, jusqu’à Aroer, qui est contre Rabba,
26 da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
Depuis Hésébon jusqu’à Ramoth, Masphé et Betonim, et depuis Manaïm jusqu’aux confins de Dabir;
27 kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
De plus, dans la vallée de Betharan, de Bethnemra, de Socoth et de Saphon, reste du royaume de Séhon, roi d’Hésébon; sa limite est aussi le Jourdain jusqu’à l’extrémité de la mer de Généreth, au-delà du Jourdain, du côté oriental.
28 Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
Voilà la possession des enfants de Gad, selon leurs familles, voilà les villes et les villages de ces familles.
29 Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
Moïse donna aussi à la demi-tribu de Manassé et à ses enfants, selon leur parenté, une possession,
30 Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
Dont voici le commencement: Depuis Manaïm, tout Basan, tous les royaumes d’Og, roi de Bazan, tous les bourgs de Jaïr qui sont en Basan, soixante villes;
31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
Et la moitié de Galaad, Astaroth et Edraï, villes du royaume d’Og, en Basan, aux enfants de Machir, fils de Manassé, c’est-à-dire à la moitié des enfants de Machir, selon leur parenté.
32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
Moïse partagea cette possession dans la plaine de Moab, au-delà du Jourdain, contre Jéricho, du côté oriental.
33 Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.
Mais à la tribu de Lévi, il ne donna pas de possession, parce que le Seigneur Dieu d’Israël est lui-même sa possession, comme il lui a dit.

< Yoshuwa 13 >