< Yoshuwa 13 >

1 Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
When Joshua was very old, Yahweh said to him, “Joshua, you are now an old man, but there is still a lot of land [for your army] to capture.
2 “Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
Here is a list of the land that remains: The Geshur region and all the area where the Philistia people-group live;
3 Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
the area where the Canaan people-group live, from the Shihor River [in the south] at the [eastern] border of Egypt, to Ekron [city] in the north; the rulers of the five [cities] of Gaza, Ashdod, Ashkelon, Gath, and Ekron; the area where the Avva people-group live,
4 Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
which is south of the area where the Canaan people-group live;
5 da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
the area where the Gebal people-group live; and all the Lebanon area east of Baal-Gad [city] at the bottom of Hermon Mountain, as far as Lebo-Hamath.
6 “Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
All the people of the Sidon people-group live in the hilly area from Lebanon to Misrephoth-Maim, but I will force them to leave that area before you Israelis arrive there. Be sure to give that area to the Israeli people when you divide the land among them, like I told you to do.
7 ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
Divide all that land among the nine Israeli tribes and half of the tribe of Manasseh, [the tribes that do not have land on the east side of the Jordan River].”
8 Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
Half of the tribe of Manasseh and the tribes of Reuben and Gad had already been told what land they would receive, because Moses, the man who served Yahweh [well], had already assigned to them the land on the east side of the Jordan [River].
9 Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
Their land extended from Aroer [town] at the Arnon River gorge to the town in the middle of the gorge. It included the whole plain from Medeba [town south] to Dibon [town].
10 da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
All the towns ruled by King Sihon were in that area. The land extended to where the Ammon people-group lived.
11 Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
The Gilead area was also there, and the regions where the people of the Geshur and Maacah people-groups lived, and all of Hermon Mountain and all the Bashan region [south] to Salecah.
12 wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
All the land ruled by Og, the king who ruled the Bashan [region], was in that land. Og was one of the last descendants of Repha; previously he had ruled in Ashtaroth and Edrei [cities], but [the armies of] Moses had defeated their armies and had taken their land from them.
13 Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
But the Israelis did not force the people of the Geshur and Maacah [people-groups] to leave their land, so they still live among the Israeli people.
14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
The tribe of Levi was the only tribe that did not get any land. Instead, just like Yahweh promised, they continued to receive [food from] the sacrifices that were given to Yahweh, the God whom the Israelis [worship], the sacrifices that were burned [on the sacred altar].
15 Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
Moses had allotted land to each clan in the tribe of Reuben.
16 Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
Their land extended from Aroer [town] near the Arnon River gorge to Medeba [town]. That included all of the plain [that is near Medeba] and the town in the middle of the gorge.
17 zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
It also included Heshbon [city] and all the nearby towns on the plain—Dibon, Bamioth-Baal, Beth-Baal-Meon,
18 Yahza, Kedemot, Mefa’at,
Jahaz, Kedemoth, Mephaath,
19 Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
Kiriathaim, Sibmah, Zereth-Shahar on the hill overlooking the valley,
20 Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
Beth-Peor, the hills in the Pisgah area, and Beth-Jeshimoth.
21 dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
That land included all the towns on the plain and all the area that King Sihon had previously ruled. But [the army of] Moses had defeated him and the rulers of the Midian people-group: Evi, Rekem, Zur, Hur, and Reba. The armies of all those rulers fought battles along with the army of Sihon, and they lived in that country.
22 Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
The Israeli army killed many people during those battles, including Balaam, [the prophet] from Beor, who tried to use magic to predict/tell what would happen in the future.
23 Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
The [western] boundary of the land that was allotted to the clans of the tribe of Reuben was the Jordan [River].
24 Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
Moses also allotted some land to each clan in the tribe of Gad.
25 Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
Their land included the Jazer [area] and all the towns of the Gilead [area]; half of the land where the Ammon people-group lived, as far as Aroer [town which is] near Rabbah [town];
26 da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
the area from Heshbon [city] to Ramath-Mizpah and Betonim [towns; the area] from Mahanaim [town] to the Debir region;
27 kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
Beth-Haram, Beth-Nimrah, Succoth, and Zaphon [cities] in the valley; and the other area that King Sihon had ruled on the east side of the Jordan River. That area extended [north] to the southern end of Galilee Lake.
28 Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
All this land, including the towns and villages, was allotted to the tribe of Gad.
29 Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
Moses also had allotted some of the land [on the east side of the Jordan River] to half of the tribe of Manasseh.
30 Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
Their land extended [north] from Mahanaim [city]. It included all the Bashan region, all the land that King Og had ruled, and all the towns in the Jair area in Bashan. Altogether that area included 60 towns.
31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
Their area also included half of the Gilead region, and the cities of Ashtaroth and Edrei where King Og had ruled. All that area was allotted to the clans descended from Manasseh’s son Makir.
32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
Moses had allotted to those tribes the land that was on the plain of the Moab [region], on the east side of the Jordan [River], across from Jericho.
33 Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.
But Moses did not allot any land to the tribe of Levi because Yahweh, the God whom we Israelis worship, promised that he himself would always provide for them.

< Yoshuwa 13 >