< Yoshuwa 13 >

1 Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
And Joshua he was old he had come in days and he said Yahweh to him you you are old you have come in days and the land it remains much very to take possession of it.
2 “Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
This [is] the land which remains all [the] territories of the Philistines and all the Geshurite[s].
3 Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
From the Shihor which - [is] on [the] face of Egypt and to [the] border of Ekron north-ward to the Canaanite[s] it is reckoned [the] five - [the] rulers of [the] Philistines the Gazite[s] and the Ashdodite[s] the Ashkelonite[s] the Gittite[s] and the Ekronite[s] and the Avvite[s].
4 Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
From [the] south all [the] land of the Canaanite[s] and Mearah which [belongs] to the Sidonians to Aphek towards to [the] border of the Amorite[s].
5 da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
And the land of the Gebalite[s] and all Lebanon [the] rising of the sun from Baal Gad under [the] mountain of Hermon to Lebo Hamath.
6 “Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
All [the] inhabitants of the hill country from Lebanon to Misrephoth Maim all [the] Sidonians I I will dispossess them from before [the] people of Israel only make fall it to Israel an inheritance just as I have commanded you.
7 ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
And therefore apportion the land this an inheritance to [the] nine the tribes and [the] half of the tribe Manasseh.
8 Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
With it the Reubenite[s] and the Gadite[s] they had received inheritance their which he had given to them Moses on [the] other side of the Jordan east-ward just as he had given to them Moses [the] servant of Yahweh.
9 Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
From Aroer which [is] on [the] edge of [the] wadi of Arnon and the city which [is] in [the] middle of the wadi and all the plain Medeba to Dibon.
10 da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
And all [the] cities of Sihon [the] king of the Amorite[s] who he reigned in Heshbon to [the] border of [the] people of Ammon.
11 Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
And Gilead and [the] territory of the Geshurite[s] and the Maacathite[s] and all [the] mountain of Hermon and all Bashan to Salecah.
12 wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
All [the] kingdom of Og in Bashan who he reigned in Ashtaroth and in Edrei he he was left one of [the] remnant of the Rephaites and he had defeated them Moses and he had dispossessed them.
13 Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
And not they dispossessed [the] people of Israel the Geshurite[s] and the Maacathite[s] and it has dwelt Geshur and Maacah in [the] midst of Israel until the day this.
14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Only to [the] tribe of the Levite[s] not he gave an inheritance [the] fire offerings of Yahweh [the] God of Israel that [was] inheritance its just as he had spoken to it.
15 Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
And he gave Moses to [the] tribe of [the] descendants of Reuben to clans their.
16 Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
And it belonged to them the territory from Aroer which [is] on [the] edge of [the] wadi of Arnon and the city which [is] in [the] middle of the wadi and all the plain at Medeba.
17 zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
Heshbon and all cities its which [are] in the plain Dibon and Bamoth Baal and Beth Baal Meon.
18 Yahza, Kedemot, Mefa’at,
And Jahaz and Kedemoth and Mephaath.
19 Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
And Kiriathaim and Sibmah and Zereth Shahar on [the] hill of the valley.
20 Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
And Beth Peor and [the] slopes of Pisgah and Beth Jeshimoth.
21 dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
And all [the] cities of the plain and all [the] kingdom of Sihon [the] king of the Amorite[s] who he reigned in Heshbon whom he had defeated Moses him - and [the] leaders of Midian Evi and Rekem and Zur and Hur and Reba [the] princes of Sihon [who] dwelt of the land.
22 Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
And Balaam [the] son of Beor the diviner they killed [the] people of Israel with the sword to slain [ones] their.
23 Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
And it was [the] border of [the] descendants of Reuben the Jordan and a territory this [was] [the] inheritance of [the] descendants of Reuben to clans their the cities and villages their.
24 Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
And he gave Moses to [the] tribe of Gad to [the] descendants of Gad to clans their.
25 Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
And it belonged to them the territory Jazer and all [the] cities of Gilead and [the] half of [the] land of [the] people of Ammon to Aroer which [is] on [the] face of Rabbah.
26 da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
And from Heshbon to Ramath Mizpah and Betonim and from Mahanaim to [the] territory of Lo Debar.
27 kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
And in the valley Beth Haram and Beth Nimrah and Succoth and Zaphon [the] remainder of [the] kingdom of Sihon [the] king of Heshbon the Jordan and a border to [the] end of [the] sea of Kinnereth [the] other side of the Jordan east-ward.
28 Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
This [was] [the] inheritance of [the] descendants of Gad to clans their the cities and villages their.
29 Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
And he gave Moses to [the] half of [the] tribe of Manasseh and it belonged to [the] half of [the] tribe of [the] descendants of Manasseh to clans their.
30 Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
And it was territory their from Mahanaim all Bashan all [the] kingdom of - Og [the] king of Bashan and all [the] villages of Jair which [are] in Bashan sixty citi[es].
31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
And [the] half of Gilead and Ashtaroth and Edrei [the] cities of [the] kingdom of Og in Bashan [belong] to [the] descendants of Makir [the] son of Manasseh to [the] half of [the] descendants of Makir to clans their.
32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
These [are that] which he gave as a possession Moses in [the] plains of Moab from [the] other side of [the] Jordan of Jericho east-ward.
33 Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.
And to [the] tribe of the Levite[s] not he gave Moses an inheritance Yahweh [the] God of Israel he [was] inheritance their just as he had spoken to them.

< Yoshuwa 13 >