< Yoshuwa 12 >

1 Waɗannan su ne sarakunan ƙasashen da Isra’ilawa suka ci da yaƙi, suka kuma mallaki ƙasarsu a gabashin Urdun, daga kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon haɗe da dukan gefen gabas na Araba.
Now these are the kings of the land, whom the men of Israel conquered. The Israelites took possession of the land on the east side of the Jordan where the sun rises, from the Valley of the Arnon River to Mount Hermon, and all the Arabah to the east.
2 Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Ya yi mulki daga Arower wadda take iyakar kwarin Arnon, daga tsakiyar kwarin har zuwa, Kogin Yabbok, wanda yake iyakar Ammonawa. Wannan ya haɗa da rabin Gileyad.
Sihon, king of the Amorites, lived in Heshbon. He ruled from Aroer, which is on the rim of the Arnon Gorge from the middle of the valley, and half of Gilead down to the Jabbok River on the border of the Ammonites.
3 Ya kuma yi mulki a kan gabashin Araba daga tekun Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri), zuwa Bet-Yeshimot da kuma kudu zuwa gangaren dutsen Fisga.
Sihon also ruled over the Arabah to the Sea of Kinnereth, to the east, to the Sea of the Arabah (the Salt Sea) eastward, all the way to Beth Jeshimoth and southward, toward the foot of the slopes of Mount Pisgah.
4 Haka ma suka ci sashen Og sarkin Bashan, ɗaya daga cikin Refahiyawa na ƙarshe da ya yi mulki a Ashtarot da Edireyi.
Og, king of Bashan, one of the remnant of the Rephaim, lived in Ashtaroth and Edrei.
5 Mulkinsa ya taso daga Dutsen Hermon, da Saleka, da dukan Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa haɗe da rabin Gileyad, zuwa kan iyakar Heshbon ta sarki Sihon.
He ruled over Mount Hermon, Salekah, and all Bashan, to the border of the people of Geshur and the Maacathites, and half of Gilead, to the border of Sihon, king of Heshbon.
6 Sai Musa, bawan Ubangiji da Isra’ilawa suka ci Sihon da Og da yaƙi. Musa bawan Ubangiji kuwa ya ba da ƙasarsu ga mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse.
Moses the servant of Yahweh, and the people of Israel had defeated them, and Moses the servant of Yahweh, gave the land as a possession to the Reubenites, the Gadites, and the half tribe of Manasseh.
7 Waɗannan su ne sarakuna da kuma ƙasashen da Yoshuwa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi a yammancin Urdun, daga Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon zuwa Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa Seyir. Yoshuwa ya raba ƙasarsu ta zama gādo ga Isra’ilawa bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
These are the kings of the land whom Joshua and the people of Israel defeated on the west side of the Jordan, from Baal Gad in the valley near Lebanon to Mount Halak near Edom. Joshua gave land to the tribes of Israel for them to possess.
8 Ƙasar ta haɗa da ƙasar kan tudu, filayen arewanci, Araba, gangaren Dutse, da jejin, da kuma Negeb, wato, ƙasashen Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa.
He gave them the hill country, the lowlands, the Arabah, the sides of the mountains, the wilderness, and the Negev—the land of the Hittites, Amorites, Canaanites, Perizzites, Hivites, and Jebusites.
9 Sarkin Yeriko, ɗaya sarkin Ai (kusa da Betel), ɗaya
The kings included the king of Jericho, the king of Ai which is beside Bethel,
10 sarkin Urushalima, ɗaya sarkin Hebron, ɗaya
the king of Jerusalem, the king of Enaim,
11 sarkin Yarmut, ɗaya sarkin Lakish, ɗaya
the king of Jarmuth, the king of Lachish,
12 sarkin Eglon, ɗaya sarkin Gezer, ɗaya
the king of Eglon, the king of Gezer,
13 sarkin Debir, ɗaya sarkin Bet-Gader, ɗaya
the king of Debir, the king of Geder,
14 sarkin Horma, ɗaya sarkin Arad, ɗaya
the king of Hormah, the king of Arad,
15 sarkin Libna, ɗaya sarkin Adullam, ɗaya
the king of Libnah, the king of Adullam,
16 sarkin Makkeda, ɗaya sarkin Betel, ɗaya
the king of Makkedah, the king of Bethel,
17 sarkin Taffuwa, ɗaya sarkin Hefer, ɗaya
the king of Tappuah, the king of Hepher,
18 sarkin Afek, ɗaya sarkin Sharon, ɗaya
the king of Aphek, the king of Lasharon,
19 sarkin Madon, ɗaya sarkin Hazor, ɗaya
the king of Madon, the king of Hazor,
20 sarkin Shimron Meron, ɗaya sarkin Akshaf, ɗaya
the king of Shimron Meron, the king of Akshaph,
21 sarkin Ta’anak, ɗaya sarkin Megiddo, ɗaya
the king of Taanach, the king of Megiddo,
22 sarkin Kedesh, ɗaya sarkin Yokneyam a Karmel, ɗaya
the king of Kedesh, the king of Jokneam in Carmel,
23 sarkin Dor (A Nafot Dor), ɗaya sarkin Goyim a Gilgal, ɗaya
the king of Dor in Naphoth Dor, the king of Goyim in Gilgal,
24 sarki Tirza, ɗaya. Duka-duka dai sarakuna talatin da ɗaya ne.
and the king of Tirzah. The number of kings was thirty-one in all.

< Yoshuwa 12 >