< Yoshuwa 11 >
1 Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
Pripetilo se je, ko je Jabín, kralj iz Hacórja, slišal te stvari, da je poslal k Jobábu, kralju Madóna in h kralju Šimróna in h kralju Ahšáfa
2 ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
in h kraljem, ki so bili na severu gora in na ravninah južno od Kinérota in v dolino in na meje Dora na zahodu
3 ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
in h Kánaancem na vzhodu in na zahodu in k Amoréjcem in k Hetejcem in k Perizéjcem in k Jebusejcem po gorah in k Hivéjcem pod Hermonom v deželi Micpa.
4 Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
In odšli so ven, oni in vse njihove vojske z njimi, mnogo ljudstva, po številu celo kakor peska, ki je na morski obali, s konji in zelo mnogimi bojnimi vozovi.
5 Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
Ko so se vsi ti kralji srečali skupaj, so prišli in se skupaj utaborili pri vodah Meróma, da se borijo zoper Izrael.
6 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
Gospod je rekel Józuetu: »Ne bodi prestrašen zaradi njih, kajti jutri ob tem času jih bom vse umorjene izročil pred Izraela. Njihovim konjem boš prerezal Ahilove tetive in njihove bojne vozove sežgal z ognjem.«
7 Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
Tako je zoper njih nenadoma prišel Józue in vse bojno ljudstvo z njim pri vodah Meróa in padli so nanje.
8 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
Gospod jih je izročil v roko Izraela, ki jih je udaril in pregnal do vélikega Sidóna in do Misrefót Majima in vzhodno k dolini Micpe in udarjali so jih, dokler niso pustili nikogar preostati.
9 Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
Józue jim je storil, kakor mu je Gospod zaukazal. Njihovim konjem je prerezal Ahilove tetive in njihove bojne vozove zažgal z ognjem.
10 A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
Józue se je ob tistem času obrnil nazaj in zavzel Hacór in njihovega kralja udaril z mečem, kajti Hacór je bil prej poglavar vseh tistih kraljestev.
11 Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
Vse duše, ki so bile v njem, so udarili z ostrino meča; popolnoma so jih uničili, tam ni ostal nihče, da diha. In Hacór je požgal z ognjem.
12 Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
Vsa mesta tistih kraljev in vse kralje izmed njih je Józue zajel in jih udaril z ostrino meča in jih popolnoma uničil, kakor je zapovedal Gospodov služabnik Mojzes.
13 Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
Toda kar se tiče mest, ki so mirovala v svoji moči, pa Izrael ni požgal nobenega izmed njih, razen samo Hacór; ki ga je požgal Józue.
14 Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
Ves plen teh mest in živino so si Izraelovi otroci vzeli za plen, toda vsakega človeka so udarili z ostrino meča, dokler jih niso uničili niti niso pustili nobenega da diha.
15 Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Kakor je Gospod zapovedal svojemu služabniku Mojzesu, tako je Mojzes zapovedal Józuetu in tako je storil Józue. Ničesar ni pustil nenarejenega, od vsega, kar je Gospod zapovedal Mojzesu.
16 Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
Tako je Józue zavzel vso tisto deželo, hribe in vso južno deželo, vso deželo Gošen, dolino in ravnino, Izraelovo goro in dolino te iste,
17 Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
torej od gore Halak, ki gre gor k Seírju, celo do Báal Gada v libanonski dolini pod goro Hermon. Zajel je vse njihove kralje, jih udaril in usmrtil.
18 Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
Józue je dolgo časa bojeval vojno z vsemi tistimi kralji.
19 Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
Tam ni bilo mesta, ki bi z Izraelovimi otroki sklenilo mir, razen Hivéjcev, prebivalcev Gibeóna. Vse druge so zavzeli v bitki.
20 Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Kajti to je bilo od Gospoda, da zakrkne njihova srca, da bi prišli v boj zoper Izrael, da bi jih lahko popolnoma uničil in da ne bi imeli naklonjenosti, temveč da bi jih lahko uničil, kakor je Gospod zapovedal Mojzesu.
21 A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
Ob tistem času je prišel Józue in iztrebil Anákovce z gora, iz Hebróna, iz Debírja, iz Anába, iz vseh Judovih gora in iz vseh Izraelovih gora. Józue jih je popolnoma uničil z njihovimi mesti.
22 Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
Nobeden izmed Anákovcev ni ostal v deželi Izraelovih otrok. Ostali so samo v Gazi, Gatu in v Ašdódu.
23 Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.
Tako je Józue zavzel celotno deželo, glede na vse, kar je Gospod rekel Mojzesu, in Józue jo je dal za dediščino Izraelu, glede na njihove oddelke po njihovih rodovih. In dežela je počivala pred vojno.