< Yoshuwa 11 >

1 Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
Et aussitôt que Jabin, Roi de Hatsor, eut appris ces choses, il envoya à Jobab Roi de Madon, et au Roi de Simron, et au Roi d'Acsaph,
2 ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
Et aux Rois qui [habitaient] vers le Septentrion, aux montagnes et dans la campagne, [vers] le Midi de Kinnaroth, et dans la plaine, et à Naphoth-Dor vers l'Occident;
3 ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
Au Cananéen qui était à l'Orient et à l'Occident, à l'Amorrhéen, à l'Héthien, au Phérésien, au Jébusien dans les montagnes, et a l'Hévien sous Hermon au pays de Mitspa.
4 Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
Ils sortirent donc et toutes leurs armées avec eux, un grand peuple, comme le sable qui est sur le bord de la mer, par leur multitude; il y avait aussi des chevaux et des chariots en fort grand nombre.
5 Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
Tous ces Rois-là s'étant donnés assignation, vinrent, et se campèrent ensemble près des eaux de Mérom, pour combattre contre Israël.
6 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
Et l'Eternel dit à Josué: Ne les crains point; car demain, environ cette même heure, je les livrerai tous, blessés à mort, devant Israël; tu couperas les jarrets à leurs chevaux, et brûleras au feu leurs chariots.
7 Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
Josué donc et tous les gens de guerre avec lui vinrent promptement contr'eux près des eaux de Mérom, et les chargèrent.
8 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
Et l'Eternel les livra entre les mains d'Israël, ils les battirent, et les poursuivirent jusqu'à Sidon la grande, et jusqu'aux eaux de Masréphoth, et jusqu'à la campagne de Mitspa, vers l'Orient, et ils les battirent tellement qu'ils n'en laissèrent échapper aucun.
9 Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
Et Josué leur fit comme l'Eternel lui avait dit; il coupa les jarrets de leurs chevaux, et brûla au feu leurs chariots.
10 A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
Et comme Josué s'en retournait en ce même temps, il prit Hatsor, et frappa son Roi avec l'épée; car Hatsor avait été auparavant la capitale de tous ces Royaumes-là.
11 Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
Ils passèrent aussi toutes les personnes qui y étaient au tranchant de l'épée, les détruisant à la façon de l'interdit; il n'y resta aucune personne vivante, et on brûla au feu Hatsor.
12 Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
Josué prit aussi toutes les villes de ces Rois-là, et tous leurs Rois, et les passa au tranchant de l'épée, [et] il les détruisit à la façon de l'interdit, comme Moïse serviteur de l'Eternel l'avait commandé.
13 Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
Mais Israël ne brûla aucune des villes, qui étaient demeurées en leur état, excepté Hatsor, que Josué brûla.
14 Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
Et les enfants d'Israël pillèrent pour eux tout le butin de ces villes-là, et les bêtes; seulement ils passèrent au tranchant de l'épée tous les hommes, jusqu'à ce qu'ils les eussent exterminés; ils n'y laissèrent de reste aucune personne vivante.
15 Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse son serviteur, ainsi Moïse l'avait commandé à Josué; et Josué le fit ainsi; de sorte qu'il n'omit rien de tout ce que l'Eternel avait commandé à Moïse.
16 Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
Josué donc prit tout ce pays-là, la montagne, et tout le pays du Midi, avec tout le pays de Gosen, la plaine, et la campagne, la montagne d'Israël, et sa plaine.
17 Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
Depuis la montagne de Halak, qui monte vers Séhir, même jusqu'à Bahal-Gad en la campagne du Liban, sous la montagne de Hermon. Il prit aussi tous leurs Rois, et les battit, et les fit mourir.
18 Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
Josué fit la guerre plusieurs jours contre tous ces Rois-là.
19 Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
Il n'y eut aucune ville qui fît la paix avec les enfants d'Israël, excepté les Héviens qui habitaient à Gabaon; ils les prirent toutes par guerre.
20 Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Car cela venait de l'Eternel qu'ils endurcissaient leur cœur pour sortir en bataille contre Israël, afin qu'il les détruisît à la façon de l'interdit, sans qu'il leur fît aucune grâce; mais qu'il les exterminât, comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse.
21 A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
En ce temps-là aussi Josué vint et extermina les Hanakins des montagnes, de Hébron, de Débir, de Hanab, et de toute montagne de Juda, et de toute montagne d'Israël; Josué, [dis-je], les détruisit à la façon de l'interdit avec leurs villes.
22 Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
Il ne resta aucun des Hanakins au pays des enfants d'Israël; il en demeura de reste seulement à Gaza, à Gath, et à Asdod.
23 Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.
Josué donc prit tout le pays, suivant tout ce que l'Eternel avait dit à Moïse, et il le donna en héritage à Israël, selon leurs portions, et leurs Tribus; et le pays fut tranquille, sans avoir guerre.

< Yoshuwa 11 >