< Yoshuwa 11 >
1 Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
And it comes to pass, when Jabin king of Hazor hears, that he sends to Jobab king of Madon, and to the king of Shimron, and to the king of Achshaph,
2 ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
and to the kings who [are] on the north in the hill-country, and in the plain south of Chinneroth, and in the low country, and in the elevations of Dor, on the west,
3 ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
[to] the Canaanite on the east, and on the west, and the Amorite, and the Hittite, and the Perizzite, and the Jebusite in the hill-country, and the Hivite under Hermon, in the land of Mizpeh—
4 Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
and they go out, they and all their camps with them, a people numerous, as the sand which [is] on the seashore for multitude, and [with] very many horse and charioteer;
5 Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
and all these kings are met together, and they come and encamp together at the waters of Merom, to fight with Israel.
6 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
And YHWH says to Joshua, “Do not be afraid of their presence, for about this time tomorrow I am giving all of them slain before Israel; hamstring their horses, and burn their chariots with fire.”
7 Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
And Joshua comes, and all the people of war with him, against them by the waters of Merom, and they suddenly fall on them;
8 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
and YHWH gives them into the hand of Israel, and they strike them and pursue them to the great Sidon, and to Misrephoth-Maim, and to the Valley of Mizpeh eastward, and they strike them, until he has not left a remnant to them;
9 Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
and Joshua does to them as YHWH commanded to him; he has hamstrung their horses, and burned their chariots with fire.
10 A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
And Joshua turns back at that time, and captures Hazor, and he has struck its king by the sword; for Hazor [was] formerly head of all these kingdoms;
11 Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
and they strike every person who [is] in it by the mouth of the sword; he has devoted—he has not left anyone breathing, and he has burned Hazor with fire;
12 Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
and all the cities of these kings, and all their kings, Joshua has captured, and he strikes them by the mouth of the sword; he devoted them, as Moses, servant of YHWH, commanded.
13 Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
Only, all the cities which are standing by their hill, Israel has not burned them—except Joshua has burned Hazor, only;
14 Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
and all the spoil of these cities, and the livestock, the sons of Israel have spoiled for themselves; only, they have struck every man by the mouth of the sword, until their destroying them; they have not left anyone breathing.
15 Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
As YHWH commanded His servant Moses, so Moses commanded Joshua, and so Joshua has done; he has not turned aside a thing of all that YHWH commanded Moses.
16 Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
And Joshua takes all this land: the hill-country, and all the south, and all the land of Goshen, and the low country, and the plain, even the hill-country of Israel and its low lands,
17 Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
from the Mount of Halak, which is going up [to] Seir, and to Ba‘al-Gad, in the Valley of Lebanon, under Mount Hermon; and he has captured all their kings, and he strikes them, and puts them to death.
18 Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
Joshua has made war with all these kings [for] many days;
19 Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
there has not been a city which made peace with the sons of Israel except the Hivite, inhabitants of Gibeon; they have taken the whole in battle;
20 Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
for it has been from YHWH to strengthen their heart, to meet in battle with Israel, in order to devote them, so that they have no grace, but in order to destroy them, as YHWH commanded Moses.
21 A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
And Joshua comes at that time, and cuts off the Anakim from the hill-country, from Hebron, from Debir, from Anab, and from all the hill-country of Judah, and from all the hill-country of Israel; Joshua has devoted them with their cities.
22 Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
There has not been Anakim left in the land of the sons of Israel; only in Gaza, in Gath, and in Ashdod, were they left.
23 Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.
And Joshua takes the whole of the land, according to all that YHWH has spoken to Moses, and Joshua gives it for an inheritance to Israel according to their divisions, by their tribes; and the land has rest from war.