< Yoshuwa 10 >
1 Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
A kad èu Adonisedek car Jerusalimski da je Isus uzeo Gaj i raskopao ga, kao što je uèinio s Jerihonom i njegovijem carem, tako da je uèinio i s Gajem i njegovijem carem, i da su Gavaonjani uèinili mir s Izrailjem i stoje usred njih,
2 Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
Uplaši se vrlo; jer Gavaon bijaše velik grad kao kakav carski grad, i bijaše veæi od Gaja, i svi ljudi u njemu bijahu hrabri.
3 Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
Zato posla Adonisedek car Jerusalimski k Oamu caru Hevronskom i k Piramu caru Jarmutskom i k Jafiji caru Lahiskom i k Daviru caru Jeglonskom, i poruèi:
4 “Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
Hodite k meni, i pomozite mi da udarimo na Gavaon, jer uèini mir s Isusom i sa sinovima Izrailjevim.
5 Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
I skupi se i poðe pet careva Amorejskih, car Jerusalimski, car Hevronski, car Jarmutski, car Lahiski, car Jeglonski, oni i sva vojska njihova, i stavši u oko pod Gavaonom poèeše ga biti.
6 Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
Tada Gavaonjani poslaše k Isusu u oko u Galgalu i rekoše: nemoj dignuti ruku svojih sa sluga svojih; hodi brzo k nama, izbavi nas i pomozi nam, jer se skupiše na nas svi carevi Amorejski koji žive u gorama.
7 Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
I izide Isus iz Galgala, on i s njim sav narod što bješe za boj, svi junaci.
8 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
I Gospod reèe Isusu: ne boj ih se; jer ih dadoh tebi u ruke, nijedan ih se neæe održati pred tobom.
9 Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
I Isus udari na njih iznenada, išavši cijelu noæ od Galgala,
10 Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
I smete ih Gospod pred Izrailjem, koji ih ljuto pobi kod Gavaona, pa ih potjera putem kako se ide u Vetoron, i sjekoše ih do Azike i do Makide.
11 Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
A kad bježahu ispred Izrailja i bijahu niz vrlet Vetoronsku, baci Gospod na njih kamenje veliko iz neba dori do Azike, te ginjahu: i više ih izgibe od kamenja gradnoga nego što ih pobiše sinovi Izrailjevi maèem.
12 A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
Tada progovori Isus Gospodu onaj dan kad Gospod predade Amorejca sinovima Izrailjevijem, i reèe pred sinovima Izrailjevijem: stani sunce nad Gavaonom, i mjeseèe nad dolinom Elonskom.
13 Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
I stade sunce i ustavi se mjesec, dokle se ne osveti narod neprijateljima svojim. Ne piše li to u knjizi istinitoga? I stade sunce nasred neba i ne naže k zapadu skoro za cio dan.
14 Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
I ne bi takoga dana ni prije ni poslije, da Gospod posluša glas èovjeèji, jer Gospod vojeva za Izrailja.
15 Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
I vrati se Isus i sav Izrailj s njim u oko u Galgal.
16 Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
A onijeh pet careva utekoše i sakriše se u peæinu kod Makide.
17 Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
I doðe glas Isusu: naðe se pet careva sakrivenijeh u peæini kod Makide.
18 Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
A Isus reèe: privalite veliko kamenje na vrata peæini, i namjestite ljude kod nje da ih èuvaju.
19 Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
A vi ne stojte, nego gonite neprijatelje svoje i bijte ostatak njihov, ne dajte im da uðu u gradove svoje, jer vam ih dade u ruke Gospod Bog vaš.
20 Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
A kad Isus i sinovi Izrailjevi prestaše biti ih u boju vrlo velikom, razbivši ih sasvijem, a koji ih ostaše živi, utekoše u tvrde gradove,
21 Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
Vrati se sav narod zdravo u oko k Isusu u Makidu, i niko ne maèe jezikom svojim na sinove Izrailjeve, ni na jednoga.
22 Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
Tada reèe Isus: otvorite vrata od one peæine, i izvedite k meni onijeh pet careva iz peæine.
23 Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
I uèiniše tako, i izvedoše k njemu onijeh pet careva iz peæine: cara Jerusalimskoga, cara Hevronskoga, cara Jarmutskoga, cara Lahiskoga, cara Jeglonskoga.
24 Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
A kad izvedoše te careve k Isusu, sazva Isus sve ljude Izrailjce, i reèe vojvodama od vojske koje bijahu išle s njim: pristupite i stanite nogama svojim na vratove ovijem carevima. I oni pristupiše i stadoše im na vratove nogama svojim.
25 Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
A Isus im reèe: ne bojte se i ne plašite se; budite slobodni i hrabri, jer æe tako uèiniti Gospod svijem neprijateljima vašim na koje zavojštite.
26 Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
Potom ih pobi Isus i pogubi ih, i objesi ih na pet drveta, i ostaše viseæi na drvetima do veèera.
27 Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
A o zahodu sunèanom zapovjedi Isus te ih skidoše s drveta i baciše ih u peæinu, u koju se bijahu sakrili, i metnuše veliko kamenje na vrata peæini, koje osta ondje do danas.
28 A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
Istoga dana uze Isus i Makidu, i sve u njoj isijeèe oštrijem maèem, i cara njezina i njih pobi, sve duše koje bjehu u njoj, ne ostavi nijednoga živa; i uèini s carem Makidskim kao što uèini s carem Jerihonskim.
29 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
Potom otide Isus i sav Izrailj s njim iz Makide u Livnu, i stade biti Livnu.
30 Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
Pa i nju predade Gospod u ruke Izrailju i cara njezina; i isijeèe sve oštrijem maèem, sve duše koje bijahu u njoj, ne ostavi u njoj nijednoga živa; i uèini s carem njezinijem kao što uèini s carem Jerihonskim.
31 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
Potom otide Isus i sav Izrailj s njim iz Livne na Lahis, i stade u oko pred njim, i stade ga biti.
32 Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
I Gospod predade Lahis u ruke Izrailju, i on ga uze sjutradan, i isijeèe sve oštrijem maèem, sve duše što bijahu u njemu, isto onako kako uèini s Livnom.
33 Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
Tada doðe Oram car Gezerski u pomoæ Lahisu; ali pobi Isus njega i narod njegov da ne osta nijedan živ.
34 Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
Potom poðe Isus i sav Izrailj s njim iz Lahisa na Jeglon, i stavši u oko prema njemu udariše na nj;
35 A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
I uzeše ga isti dan, i isjekoše sve oštrijem maèem; sve duše što bijahu u njemu pobi taj dan isto onako kako uèini s Lahisom.
36 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
Potom se podiže Isus i sav Izrailj s njim iz Jeglona na Hevron, i stadoše ga biti;
37 Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
I uzeše ga i isjekoše oštrijem maèem, i cara njegova i sve gradove njegove, sve duše što bijahu u njima; ne ostavi nijednoga živa isto onako kako uèini s Jeglonom; zatr ga sa svijem dušama što bijahu u njemu.
38 Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
Potom se obrati Isus i sav Izrailj s njim na Davir, i stade ga biti;
39 suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
I uze ga i cara njegova i sve gradove njegove, i isjekoše ih oštrijem maèem i zgubiše sve duše što bijahu u njima; ne ostavi nijednoga živa; kao što uèini s Hevronom, tako uèini s Davirom i carom njegovijem, i kao što uèini s Livnom i carem njezinijem.
40 Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
Tako pobi Isus svu zemlju, gore i južnu stranu i ravnice i doline, i sve careve njihove; ne ostavi nijednoga živa, nego sve duše žive zgubi, kao što bješe zapovjedio Gospod Bog Izrailjev.
41 Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
I pobi ih Isus od Kadis-Varnije do Gaze, i svu zemlju Gosensku do Gavaona.
42 Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
A sve te careve i zemlju njihovu uze Isus ujedanput; jer Gospod Bog Izrailjev vojevaše za Izrailja.
43 Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.
Potom se vrati Isus i sav Izrailj s njim u oko u Galgal.