< Yoshuwa 10 >

1 Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
Or quand Adoni-tsédek, Roi de Jérusalem, eut entendu que Josué avait pris Haï, et qu'il l'avait entièrement détruite à la façon de l'interdit, ayant fait à Haï et à son Roi, comme il avait fait à Jérico et à son Roi, et que les habitants de Gabaon avaient fait la paix avec les Israélites, et étaient parmi eux;
2 Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
On craignit beaucoup, parce que Gabaon était une grande ville, comme une ville Royale, et elle était plus grande que Haï; et [parce que] tous ses hommes étaient forts.
3 Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
C'est pourquoi Adoni-tsédek, Roi de Jérusalem, envoya vers Horam Roi de Hébron, et vers Biréam, Roi de Jarmuth, et vers Japhiah, Roi de Lakis, et vers Débir, Roi de Héglon, pour leur dire:
4 “Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
Montez vers moi, et donnez-moi du secours afin que nous frappions Gabaon; car elle a fait la paix avec Josué, et avec les enfants d'Israël.
5 Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
Ainsi cinq Rois des Amorrhéens, [savoir], le Roi de Jérusalem, le Roi de Hébron, le Roi de Jarmuth, le Roi de Lakis, et le Roi de Héglon, s'assemblèrent et montèrent eux et toutes leurs armées, et se campèrent contre Gabaon, et lui firent la guerre.
6 Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
C'est pourquoi ceux de Gabaon envoyèrent à Josué au camp à Guilgal, en disant: Ne retire point tes mains de tes serviteurs; monte promptement vers nous, et nous garantis, et donne-nous du secours; car tous les Rois des Amorrhéens qui habitent aux montagnes, se sont assemblés contre nous.
7 Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
Josué donc monta de Guilgal, et avec lui tout le peuple [qui était] propre à la guerre, et tous les hommes forts et vaillants.
8 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
Et l'Eternel dit à Josué: Ne les crains point; car je les ai livrés entre tes mains, et aucun d'eux ne subsistera devant toi.
9 Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
Josué donc vint promptement à eux; [et] monta de Guilgal toute la nuit.
10 Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
Et l'Eternel les mit en déroute devant Israël, qui en fit un grand carnage près de Gabaon; et les poursuivit par le chemin de la montagne de Beth-horon, et les battit jusqu'à Hazéka, et jusqu'à Makkéda.
11 Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
Et comme ils s'enfuyaient de devant Israël, et qu'ils étaient à la descente de Beth-horon, l'Eternel jeta des cieux sur eux de grosses pierres jusqu'à Hazéka, dont ils moururent; et il y en eut encore plus de ceux qui moururent des pierres de grêle, que de ceux que les enfants d'Israël tuèrent avec l'épée.
12 A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
Alors Josué parla à l'Eternel, le jour que l'Eternel livra l'Amorrhéen aux enfants d'Israël, et dit en la présence d'Israël: Soleil, arrête-toi sur Gabaon, et toi Lune, sur la vallée d'Ajalon.
13 Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
Et le soleil s'arrêta, et la lune aussi s'arrêta, jusqu'à ce que le peuple se fût vengé de ses ennemis. Ceci n'est-il pas écrit au Livre du Droiturier? Le soleil donc s'arrêta au milieu des cieux et ne se hâta point de se coucher environ un jour entier.
14 Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
Et il n'y a point eu de jour semblable à celui-là, devant ni après, l'Eternel exauçant la voix d'un homme; car l'Eternel combattait pour les Israélites.
15 Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
Et Josué et tout Israël avec lui, s'en retourna au camp à Guilgal.
16 Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
Au reste ces cinq Rois-là s'étaient enfuis, et s'étaient cachés dans une caverne à Makkéda.
17 Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
Et on avait rapporté à Josué, en disant: On a trouvé les cinq Rois cachés dans une caverne à Makkéda.
18 Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
Et Josué avait dit: Roulez de grandes pierres à l'entrée de la caverne, mettez près d'elle quelques hommes pour les garder.
19 Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
Mais vous, ne vous arrêtez point, poursuivez vos ennemis, et les défaites jusqu'au dernier, [et] ne les laissez point entrer dans leurs villes; car l'Eternel votre Dieu les a livrés en vos mains.
20 Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
Et quand Josué avec les enfants d'Israël eut achevé d'en faire une très grande boucherie, jusqu'à les détruire entièrement, et que ceux d'entr'eux qui étaient échappés se furent retirés dans les villes fermées de murailles;
21 Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
Tout le peuple retourna en paix au camp vers Josué à Makkéda; [et] personne ne remua sa langue contre aucun des enfants d'Israël.
22 Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
Alors Josué dit: Ouvrez l'entrée de la caverne, et amenez-moi ces cinq Rois hors de la caverne.
23 Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
Et ils le firent ainsi, et ils amenèrent hors de la caverne ces cinq Rois: le Roi de Jérusalem, le Roi de Hébron, le Roi de Jarmuth, le Roi de Lakis et le Roi de Héglon.
24 Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
Et après qu'ils eurent amené à Josué ces cinq Rois hors de la caverne, Josué appela tous les hommes d'Israël, et dit aux Capitaines des gens de guerre qui étaient allés avec lui: Approchez-vous, mettez vos pieds sur le cou de ces Rois; et ils s'approchèrent, et mirent leurs pieds sur leur cou.
25 Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
Alors Josué leur dit: Ne craignez point, et ne soyez point effrayés, fortifiez-vous, et vous renforcez; car l'Eternel fera ainsi à tous vos ennemis contre lesquels vous combattez.
26 Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
Et après cela Josué les frappa, et les fit mourir, et les fit pendre à cinq potences; et ils demeurèrent pendus à ces potences jusqu'au soir.
27 Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
Et comme le soleil se couchait Josué fit commandement qu'on les ôtât de ces potences, et on les jeta dans la caverne où ils s'étaient cachés; et on mit à l'entrée de la caverne de grandes pierres [qui y sont demeurées] jusqu'à ce jour.
28 A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
Josué prit aussi en ce même jour Makkéda, et la frappa au tranchant de l'épée, et défit à la façon de l'interdit son Roi et ses [habitants], et ne laissa échapper aucune personne qui fût dans cette ville; et il fit au Roi de Makkéda comme il avait fait au Roi de Jérico.
29 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
Après cela Josué et tout Israël avec lui passa de Makkéda à Libna, et fit la guerre à Libna.
30 Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
Et l'Eternel la livra aussi entre les mains d'Israël, avec son Roi, et il la frappa au tranchant de l'épée, et ne laissa échapper aucune personne qui fût dans cette ville; et il fit à son Roi comme il avait fait au Roi de Jérico.
31 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
Ensuite Josué et tout Israël avec lui passa de Libna à Lakis, et se campa devant elle, et lui fit la guerre.
32 Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
Et l'Eternel livra Lakis entre les mains d'Israël, qui la prit le deuxième jour, et la frappa au tranchant de l'épée, et toutes les personnes qui étaient dedans, comme il avait fait à Libna.
33 Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
Alors Horam Roi de Guézer monta pour secourir Lakis; et Josué le frappa, lui et son peuple, de sorte qu'il n'en laissa pas échapper un seul homme.
34 Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
Après cela Josué et tout Israël avec lui passa de Lakis à Héglon; et ils se campèrent devant elle, et lui firent la guerre;
35 A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
Et ils la prirent ce jour-là même, et la frappèrent au tranchant de l'épée; et [Josué] défit à la façon de l'interdit en ce même jour-là toutes les personnes qui y étaient, comme il avait fait à Lakis.
36 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
Puis Josué et tout Israël avec lui monta d'Héglon à Hébron, et ils lui firent la guerre.
37 Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
Et ils la prirent, et la frappèrent au tranchant de l'épée, avec son Roi, et toutes ses villes, et toutes les personnes qui y étaient; il n'en laissa échapper aucune, comme il avait fait à Héglon; et il la défit à la façon de l'interdit, et toutes les personnes qui y étaient.
38 Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
Ensuite Josué et tout Israël avec lui rebroussa chemin vers Débir, et ils lui firent la guerre.
39 suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
Et il la prit avec son Roi, et toutes ses villes; et ils les frappèrent au tranchant de l'épée, et défirent à la façon de l'interdit toutes les personnes qui y étaient; il n'en laissa échapper aucune. Il fit à Débir et à son Roi comme il avait fait à Hébron, et comme il avait fait à Libna et à son Roi.
40 Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
Josué donc frappa tout ce pays-là, la montagne, et le Midi, et la plaine, et les pentes des montagnes, et tous leurs Rois; il n'en laissa échapper aucun; et il défit à la façon de l'interdit toutes les personnes vivantes, comme l'Eternel le Dieu d'Israël l'avait commandé.
41 Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
[Ainsi] Josué les battit depuis Kadès-barné jusqu'à Gaza, et tout le pays de Gosen, jusqu'à Gabaon.
42 Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
Il prit donc tout à la fois ces Rois-là et leur pays; parce que l'Eternel, le Dieu d'Israël, combattait pour Israël.
43 Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.
Après quoi Josué et tout Israël avec lui s'en retournèrent au camp à Guilgal.

< Yoshuwa 10 >