< Yoshuwa 10 >

1 Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
And it was when heard Adoni-Zedek [the] king of Jerusalem that he had captured Joshua Ai and he had totally destroyed it just as he had done to Jericho and to king its so he had done to Ai and to king its and that they had made peace [the] inhabitants of Gibeon with Israel and they were in midst their.
2 Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
And they were afraid very for [was] a city great Gibeon like one of [the] cities of royalty and for it [was] great more than Ai and all men its [were] warriors.
3 Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
And he sent Adoni-Zedek [the] king of Jerusalem to Hoham [the] king of Hebron and to Piram [the] king of Jarmuth and to Japhia [the] king of Lachish and to Debir [the] king of Eglon saying.
4 “Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
Come up to me and help me so we may attack Gibeon for it has made peace with Joshua and with [the] people of Israel.
5 Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
And they gathered and they went up [the] five - [the] kings of the Amorite[s] [the] king of Jerusalem [the] king of Hebron [the] king of Jarmuth [the] king of Lachish [the] king of Eglon they and all armies their and they encamped on Gibeon and they waged war on it.
6 Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
And they sent [the] men of Gibeon to Joshua to the camp Gilgal towards saying may not you let drop hands your from servants your come up to us quickly and save! us and help us for they have gathered together against us all [the] kings of the Amorite[s] [the] inhabitants of the hill country.
7 Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
And he went up Joshua from Gilgal he and all [the] people of war with him and all [the] mighty [men] of strength.
8 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
And he said Yahweh to Joshua may not you be afraid from them for in hand your I have given them not he will make a stand anyone from them in face your.
9 Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
And he came to them Joshua suddenly all the night he had gone up from Gilgal.
10 Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
And he routed them Yahweh before Israel and he struck down them a defeat great at Gibeon and he pursued them [the] direction of [the] ascent of Beth Horon and he struck down them to Azekah and to Makkedah.
11 Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
And it was when fled they - from before Israel they [were] at [the] descent of Beth Horon and Yahweh he threw on them stones large from the heavens to Azekah and they died [were] many [those] who they died by [the] stones of the hail more than [those] whom they killed [the] people of Israel with the sword.
12 A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
Then he spoke Joshua to Yahweh on [the] day delivered up Yahweh the Amorite[s] before [the] people of Israel and he said - to [the] eyes of Israel O sun at Gibeon be still and O moon in [the] valley Aijalon.
13 Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
And it was still the sun and [the] moon it stood still until it avenged itself on [the] nation enemies its ¿ not [is] it written on [the] scroll of Jashar and it stood still the sun in [the] middle of the heavens and not it hastened to go about a day complete.
14 Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
And not it has been like the day that before it and after it to listen Yahweh to [the] voice of a man for Yahweh [was] fighting for Israel.
15 Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
And he returned Joshua and all Israel with him to the camp Gilgal towards.
16 Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
And they fled [the] five the kings these and they hid themselves in the cave at Makkedah.
17 Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
And it was told to Joshua saying they have been found [the] five the kings hidden in the cave at Makkedah.
18 Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
And he said Joshua roll stones large into [the] mouth of the cave and appoint over it men to guard them.
19 Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
And you may not you delay pursue after enemies your and you will attack in [the] rear them may not you permit them to go into cities their for he has given them Yahweh God your in hand your.
20 Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
And it was when finished Joshua and [the] people of Israel to strike down them a defeat great very until were finished they and the survivors they survived of them and they went into [the] cities of fortification.
21 Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
And they returned all the people to the camp to Joshua Makkedah in peace not he sharpened to [the] people of Israel to anyone tongue his.
22 Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
And he said Joshua open [the] mouth of the cave and bring out to me [the] five the kings these from the cave.
23 Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
And they did thus and they brought out to him [the] five the kings these from the cave - [the] king of Jerusalem [the] king of Hebron [the] king of Jarmuth [the] king of Lachish [the] king of Eglon.
24 Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
And it was when brought out they the kings these to Joshua and he summoned Joshua every man of Israel and he said to [the] commanders of [the] men of war who had gone with him draw near put feet your on [the] necks of the kings these and they drew near and they put feet their on necks their.
25 Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
And he said to them Joshua may not you be afraid and may not you be dismayed be strong and be bold for thus he will do Yahweh to all enemies your whom you [are] fighting them.
26 Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
And he struck them Joshua after thus and he killed them and he hanged them on five trees and they were hanged on the trees until the evening.
27 Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
And it was to [the] time of - [the] going of the sun he commanded Joshua and people took down them from on the trees and they threw them into the cave where they had hidden themselves there and they put stones large over [the] mouth of the cave until [the] substance of the day this.
28 A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
And Makkedah he captured Joshua on the day that and he struck it to [the] mouth of [the] sword and king its he totally destroyed them and every person who [was] in it not he left a survivor and he did to [the] king of Makkedah just as he had done to [the] king of Jericho.
29 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
And he passed on Joshua and all Israel with him from Makkedah Libnah and he engaged in battle with Libnah.
30 Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
And he gave Yahweh also it in [the] hand of Israel and king its and he struck it to [the] mouth of [the] sword and every person who [was] in it not he left in it a survivor and he did to king its just as he had done to [the] king of Jericho.
31 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
And he passed on Joshua and all Israel with him from Libnah Lachish towards and he encamped on it and he engaged in battle against it.
32 Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
And he gave Yahweh Lachish in [the] hand of Israel and he captured it on the day second and he struck it to [the] mouth of [the] sword and every person who [was] in it according to all that he had done to Libnah.
33 Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
Then he came up Horam [the] king of Gezer to help Lachish and he attacked him Joshua and people his until not he had left to him a survivor.
34 Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
And he passed on Joshua and all Israel with him from Lachish Eglon towards and they encamped on it and they engaged in battle on it.
35 A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
And they captured it on the day that and they struck it to [the] mouth of [the] sword and every person who [was] in it on the day that he totally destroyed according to all that he had done to Lachish.
36 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
And he went up Joshua and all Israel with him from Eglon Hebron towards and they engaged in battle on it.
37 Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
And they captured it and they struck it to [the] mouth of [the] sword and king its and all cities its and every person who [was] in it not he left a survivor according to all that he had done to Eglon and he totally destroyed it and every person who [was] in it.
38 Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
And he turned back Joshua and all Israel with him Debir towards and he engaged in battle on it.
39 suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
And he captured it and king its and all cities its and they struck them to [the] mouth of [the] sword and they totally destroyed every person who [was] in it not he left a survivor just as he had done to Hebron so he did to Debir and to king its and just as he had done to Libnah and to king its.
40 Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
And he defeated Joshua all the land the hill country and the Negev and the Shephelah and the slopes and all kings their not he left a survivor and every breathing thing he totally destroyed just as he had commanded Yahweh [the] God of Israel.
41 Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
And he struck down them Joshua from Kadesh Barnea and to Gaza and all [the] land of Goshen and to Gibeon.
42 Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
And all the kings these and land their he captured Joshua time one for Yahweh [the] God of Israel [was] fighting for Israel.
43 Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.
And he returned Joshua and all Israel with him to the camp Gilgal towards.

< Yoshuwa 10 >