< Yunana 1 >

1 Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
Ilizwi leNkosi laselifika kuJona indodana kaAmithayi, lisithi:
2 “Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
Sukuma, uye eNineve, umuzi omkhulu, umemeze umelene lawo; ngoba ububi babo benyukele phambi kwami.
3 Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
Kodwa uJona wasukuma ukuze abalekele eTarshishi esuka ebusweni beNkosi, wehlela eJopha, wathola umkhumbi oya eTarshishi, wanika imali yawo, wehlela kuwo, ukuze ahambe labo eTarshishi, asuke ebusweni beNkosi.
4 Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
Kodwa iNkosi yaphosa umoya omkhulu elwandle; kwasekusiba lesiphepho esikhulu elwandle, okungangokuthi umkhumbi wacatshangelwa ukwephuka.
5 Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
Abatshayeli bomkhumbi basebesesaba, bakhala, ngulowo lalowo kunkulunkulu wakhe, baphosela olwandle izimpahla ezazisemkhunjini, ukuwenza ube lula kuzo. Kodwa uJona wayehlele emaceleni omkhumbi, walala, waba lobuthongo obukhulu.
6 Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
Ngakho induna yomkhumbi yasondela kuye, yathi kuye: Ulani wena olobuthongo obukhulu? Vuka, ubize kuNkulunkulu wakho; mhlawumbe lowoNkulunkulu angasikhumbula, ukuze singabhubhi.
7 Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
Basebesithi, ngulowo kumngane wakhe: Wozani senze inkatho yokuphosa, ukuze sazi ukuthi kungenxa kabani lobububi buphezu kwethu. Basebesenza inkatho yokuphosa; inkatho yasiwela phezu kukaJona.
8 Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
Basebesithi kuye: Akusitshele ukuthi kungenxa kabani lobububi buphezu kwethu. Umsebenzi wakho uyini? Njalo uvela ngaphi? Yiliphi ilizwe lakini? Njalo ungowasiphi isizwe?
9 Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
Wasesithi kubo: NgingumHebheru, ngiyayesaba iNkosi, uNkulunkulu wamazulu, owenza ulwandle lomhlabathi owomileyo.
10 Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
Amadoda asesesaba ngokwesaba okukhulu, athi kuye: Ukwenzeleni lokhu? Ngoba amadoda akwazi ukuthi ubalekile ebusweni beNkosi, ngoba wayesewatshelile.
11 Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
Asesithi kuye: Senzeni kuwe ukuze ulwandle luthule kithi? Ngoba ulwandle lwaqhubeka lwaba lesiphepho esikhulu.
12 Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
Wasesithi kiwo: Ngiphakamisani, lingiphosele olwandle; ngalokho ulwandle luzalithulela; ngoba ngiyazi ukuthi lesisiphepho esikhulu siphezu kwenu ngenxa yami.
13 Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
Kodwa amadoda agwedla ngamandla ukuze awubuyisele umkhumbi emhlabathini owomileyo, kodwa ehluleka, ngoba ulwandle lwaqhubeka lwaba lesiphepho lumelene lawo.
14 Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
Ngakho akhala eNkosini, athi: Siyakuncenga, Nkosi, kasingabhubhi ngenxa yempilo yalumuntu, ungabeki phezu kwethu igazi elingelacala; ngoba wena, Nkosi, wenzile njengokukuthokozisayo.
15 Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
Asephakamisa uJona, amphosela elwandle; ulwandle lwaselusima ekuvubekeni kwalo.
16 Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
Amadoda aseyesaba iNkosi ngokwesaba okukhulu, anikela umhlatshelo eNkosini, afunga izifungo.
17 Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.
Njalo iNkosi yayimise inhlanzi enkulu ukuze imginye uJona; njalo uJona waba semathunjini enhlanzi insuku ezintathu lobusuku obuthathu.

< Yunana 1 >