< Yunana 4 >
1 Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
Dette gjorde Jona ovleg vondt, og han vart brennande harm.
2 Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
Han bad då til Herren og sagde: «Å Herre, var det ikkje dette eg tenkte, då eg endå var i mitt land? Difor flydde eg so snøgt til Tarsis; for eg visste du er ein nådig og miskunnsam Gud, langmodig og rik på miskunn, og angrar det vonde.
3 Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
So tak no, Herre, livet mitt ifrå meg! For eg vil heller døy enn liva.»
4 Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
Då sagde Herren: «Hev du grunn til å harmast?»
5 Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
Og Jona gjekk ut or byen og sette seg austanfor byen. Der gjorde han seg ei hytta og sette seg der i skuggen, og vilde sjå korleis det gjekk med byen.
6 Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
Då let Herren Gud ein kikajon veksa upp yver Jona, til å skyggja yver hovudet hans og fria honom ifrå hans mismod; og Jona fann stor gleda i kikajonen.
7 Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
Men næste dag, då morgonroden rann, sende Gud ein makk, som stakk kikajonen so han visna.
8 Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
Då soli rann, sende Gud ein brennande austanvind, og soli stakk Jona på hovudet so han ormegtast. Han ynskte då å få døy og sagde: «Eg vil heller døy enn liva.»
9 Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
Men Gud sagde til Jona: «Hev du grunn til å harmast for kikajonen skuld?» Han svara: «Eg hev grunn til å harmast til dauden.»
10 Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
Då sagde Herren: «Du ynkast yver kikajonen, som du ikkje hev havt møda med og ikkje hev ale upp, som kom til på ei natt og gjekk til grunns etter ei natt;
11 Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”
og so skulde ikkje eg ynkast yver Nineve, den store byen, der det finst meir enn eit hundrad og tjuge tusund menneskje som ikkje kann skilja millom høgre og vinstre, og mange dyr!»