< Yunana 4 >

1 Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
Kodwa kwaba kubi kakhulukazi kuJona, wathukuthela yena.
2 Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
Wasekhuleka eNkosini, wathi: Ngiyakuncenga, Nkosi, leli lalingesilo ilizwi lami ngiseselizweni lakithi yini? Ngenxa yalokhu ngandulela ngokubalekela eTarshishi; ngoba ngangisazi ukuthi wena unguNkulunkulu olomusa lolesihawu, ophuza ukuthukuthela, omkhulu ngothando, njalo ozisola ngokubi.
3 Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
Ngakho-ke, Nkosi, susa, ngiyakuncenga, impilo yami kimi, ngoba kungcono kimi ukufa kulokuphila.
4 Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
INkosi yasisithi: Wenza kuhle yini ngokuthukuthela kwakho?
5 Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
UJona wasephuma emzini, wahlala ngasempumalanga komuzi, wazenzela idumba khona, wahlala ngaphansi kwalo emthunzini, aze abone okuzakwenzakala kuwo umuzi.
6 Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
INkosi uNkulunkulu yasimisa umhlafutho, yawukhulisa ngaphezu kukaJona, ukuze ube ngumthunzi phezu kwekhanda lakhe, ukumkhulula kubuhlungu bakhe. UJona wasethokoza ngenxa yomhlafutho ngentokozo enkulu.
7 Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
Kodwa uNkulunkulu wamisa impehlane ekuveleni kokusa kusisa, yatshaya umhlafutho, waze wabuna.
8 Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
Kwasekusithi ekuphumeni kwelanga, uNkulunkulu wamisa umoya wempumalanga otshisayo; njalo ilanga latshaya phezu kwekhanda likaJona, waze waphela amandla; wafisa emphefumulweni wakhe ukuthi afe, wathi: Kungcono kimi ukufa kulokuphila.
9 Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
UNkulunkulu wasesithi kuJona: Wenza kuhle yini ngokuthukuthela kwakho ngenxa yomhlafutho? Wasesithi: Ngenza kuhle ngokuthukuthela kwami kuze kube sekufeni.
10 Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
INkosi yasisithi: Wena ube lozwelo phezu komhlafutho ongawutshikatshikelanga, ongawukhulisanga; owaba khona ngobusuku bunye, wabhubha ngobusuku bunye.
11 Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”
Mina-ke ngabe kangihawukeli yini iNineve, umuzi omkhulu, okuthi kuwo kulabantu abedlula izinkulungwane ezilikhulu lamatshumi amabili abangaziyo ukwehlukanisa phakathi kwesandla sabo sokunene lesandla sabo sokhohlo, kanye lenkomo ezinengi?

< Yunana 4 >