< Yunana 4 >
1 Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
But this displeased Jonah exceedingly, and he was very angry.
2 Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
And he prayed to Jehovah and said, Ah! Jehovah, was not this what I said, when I was yet in my own country? Therefore I made haste to flee to Tarshish. For I knew that thou art a gracious and merciful God, slow to anger and abundant in mercy, and that thou repentest of a threatened evil.
3 Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
And now, O Jehovah, take, I pray thee, my life from me! for it is better for me to die than to live.
4 Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
And Jehovah said, Is it right that thou shouldst be angry?
5 Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
Now Jonah had gone out of the city, and had sat on the east side of the city, and had made himself a booth there, and had sat under it in the shade, till he should see what would become of the city.
6 Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
And God, Jehovah, appointed a gourd; and it grew up over Jonah to be a shadow over his head, to deliver him from his distress. And Jonah was exceedingly glad of the gourd.
7 Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
But God appointed a worm when the morning rose the next day, and it smote the gourd so that it withered.
8 Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
And when the sun arose, God appointed a sultry east wind; and the sun beat upon the head of Jonah, and he was faint, and he asked for himself death, and said, It is better for me to die than to live.
9 Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
And God said to Jonah, Is it right that thou shouldst be angry for the gourd? And he said, It is right that I should be angry even to death.
10 Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
And Jehovah said, Thou hast had pity on the gourd for which thou hast not labored, and which thou madest not to grow, which grew up in a night and perished in a night;
11 Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”
and should not I spare Nineveh, the great city, wherein are more than a hundred and twenty thousand persons that cannot discern between their right hand and their left hand, and also many cattle?