< Yunana 4 >

1 Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
And Jonah was afflicted with a great affliction, and he was angry.
2 Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
And he prayed to the Lord, and he said, “I beg you, Lord, was this not my word, when I was still in my own land? Because of this, I knew beforehand to flee into Tarshish. For I know that you are a lenient and merciful God, patient and great in compassion, and forgiving despite ill will.
3 Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
And now, Lord, I ask you to take my life from me. For it is better for me to die than to live.”
4 Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
And the Lord said, “Do you really think you are right to be angry?”
5 Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
And Jonah went out of the city, and he sat opposite the east of the city. And he made himself a shelter there, and he was sitting under it in the shadow, until he might see what would befall the city.
6 Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
And the Lord God prepared an ivy, and it ascended over the head of Jonah so as to be a shadow over his head, and to protect him (for he had labored hard). And Jonah rejoiced because of the ivy, with great rejoicing.
7 Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
And God prepared a worm, when dawn approached on the next day, and it struck the ivy, and it dried up.
8 Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
And when the sun had risen, the Lord ordered a hot and burning wind. And the sun beat down on the head of Jonah, and he burned. And he petitioned for his soul that he might die, and he said, “It is better for me to die than to live.”
9 Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
And the Lord said to Jonah, “Do you really think that you are right to be angry because of the ivy?” And he said, “I am right to be angry even unto death.”
10 Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
And the Lord said, “You grieve for the ivy, for which you have not labored and which you did not cause to grow, though it had been born during one night, and during one night perished.
11 Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”
And shall I not spare Nineveh, the great city, in which there are more than one hundred and twenty thousand men, who do not know the difference between their right and their left, and many beasts?”

< Yunana 4 >