< Yunana 3 >

1 Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
And the word of the Lord was maad the secounde tyme to Jonas, and seide, Rise thou,
2 “Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
and go in to Nynyue, the greet citee, and preche thou in it the prechyng which Y speke to thee.
3 Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
And Jonas roos, and wente in to Nynyue, bi the word of the Lord. And Nynyue was a greet citee, of the iurnei of thre daies.
4 A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
And Jonas bigan for to entre in to the citee, bi the iornei of o dai, and criede, and seide, Yit fourti daies, and Nynyue schal be `turned vpsodoun.
5 Mutanen Ninebe kuwa suka gaskata Allah. Aka yi shela a yi azumi, sai dukansu daga babba har zuwa ƙaraminsu, suka sa tufafin makoki.
And men of Nynyue bileueden to the Lord, and prechiden fastyng, and weren clothid with sackis, fro the more `til to the lesse.
6 Da saƙon Yunana ya kai kunnen sarkin Ninebe, sai ya tashi daga kujerar mulkinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.
And the word cam til to the kyng of Nynyue; and he roos of his seete, and castide awei his clothing fro him, and was clothid with a sak, and sat in aische.
7 Sai ya yi umarni a Ninebe cewa, “Bisa ga umarnin sarki da fadawansa. “Kada a bar wani mutum ko dabba, garke ko shannu, su ɗanɗana wani abu; kada a bari su ci ko su sha.
And he criede, and seide in Nynyue of the mouth of the kyng and of `his princis, `and seide, Men, and werk beestis, and oxun, and scheep taaste not ony thing, nether be fed, nether drynke watir.
8 Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
And men be hilid with sackis, and werk beestis crie to the Lord in strengthe; `and be a man conuertid fro his yuel weie, and fro wickidnesse that is in the hondis of hem.
9 Wa ya sani? Ko Allah zai ji tausayinmu da kuma juyayinmu yă janye zafin fushinsa don kada mu hallaka.”
Who woot, if God be conuertid, and foryyue, and be turned ayen fro woodnesse of his wraththe, and we schulen not perische?
10 Da Allah ya ga abin da suka yi, da kuma yadda suka juya daga mugayen hanyoyinsu sai ya ji tausayinsu, bai kawo hallaka a kansu yadda ya yi shirin yi ba.
And God sai the werkis of hem, that thei weren conuertid fro her yuel weie; and God hadde merci on the malice which he spac, that he schulde do to hem, and did not.

< Yunana 3 >