< Yunana 3 >
1 Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
The word of Yahweh came to Jonah a second time, saying,
2 “Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
“Get up, go to Nineveh, that great city, and proclaim to it the message that I command you to give.”
3 Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
So Jonah got up and went to Nineveh in obedience to the word of Yahweh. Now Nineveh was a very large city, one of three days' journey.
4 A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
Jonah began to enter the city and after a day's journey he called out and said, “In forty days Nineveh will be overthrown.”
5 Mutanen Ninebe kuwa suka gaskata Allah. Aka yi shela a yi azumi, sai dukansu daga babba har zuwa ƙaraminsu, suka sa tufafin makoki.
The people of Nineveh believed God and they proclaimed a fast. They all put on sackcloth, from the greatest of them down to the least of them.
6 Da saƙon Yunana ya kai kunnen sarkin Ninebe, sai ya tashi daga kujerar mulkinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.
Soon the news reached the king of Nineveh. He rose up from his throne, took off his robe, covered himself with sackcloth, and sat in ashes.
7 Sai ya yi umarni a Ninebe cewa, “Bisa ga umarnin sarki da fadawansa. “Kada a bar wani mutum ko dabba, garke ko shannu, su ɗanɗana wani abu; kada a bari su ci ko su sha.
He sent out a proclamation that said, “In Nineveh, by the authority of the king and his nobles, let neither man nor animal, herd nor flock, taste anything. Let them not eat, nor drink water.
8 Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
But let both man and animal be covered with sackcloth and let them cry out loudly to God. Let every one turn from his evil way and from the violence that is in his hands.
9 Wa ya sani? Ko Allah zai ji tausayinmu da kuma juyayinmu yă janye zafin fushinsa don kada mu hallaka.”
Who knows? God may relent and change his mind and turn away from his fierce anger so that we do not perish.”
10 Da Allah ya ga abin da suka yi, da kuma yadda suka juya daga mugayen hanyoyinsu sai ya ji tausayinsu, bai kawo hallaka a kansu yadda ya yi shirin yi ba.
God saw what they did, that they turned from their evil ways. So then God changed his mind about the punishment that he had said he would do to them, and he did not do it.