< Yunana 2 >
1 Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
Then prayed Jonah, unto Yahweh, his God, —out of the belly of the fish;
2 Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol )
and said—I cried—out of my distress—unto Yahweh, and he answered me, —Out of the belly of hades, called I, Thou didst hear my voice. (Sheol )
3 Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
For thou hast cast me into the deep, into the heart of the seas, and, a flood, enveloped me, —All thy breakers and thy rolling waves, over me, passed.
4 Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
And, I, said, I am driven out from before thine eyes, —Yet will I again have regard unto thy holy temple:
5 Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
The waters, encompassed me, to the peril of my life, The roaring deep, enveloped me, —The sea-weed, was wrapped about my head:
6 Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
To the roots of the mountains, went I down, As for the earth, her bars, were about me, age-abidingly, —Then didst thou bring up—out of the pit—my life, O Yahweh my God.
7 “Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
When my soul, darkened itself over me, Yahweh, I remembered, —and my prayer, came in unto thee, unto thy holy temple.
8 “Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
They who take heed to the vanities of falsehood, do, their own lovingkindness, forsake.
9 Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
But, I, with the voice of praise, will sacrifice unto thee, What I have vowed, I will pay, —Salvation, belongeth to Yahweh!
10 Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.
So then Yahweh spake unto the fish, —and it vomited out Jonah, upon the dry land.