< Yunana 2 >

1 Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
Og Jonas bad til Herren sin Gud fra Fiskens Liv,
2 Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol h7585)
og han sagde: Jeg raabte til Herren ud af min Angest, og han svarede mig; jeg, skreg fra Dødsrigets Skød, du hørte min Røst. (Sheol h7585)
3 Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
Du kastede mig i Dybet, midt i Havet, og Strømmen omgav mig; alle dine Vover og dine Bølger gik over mig.
4 Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
Og jeg sagde: Jeg er udstødt fra dine Øjne, men jeg skal atter skue hen til dit hellige Tempel.
5 Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
Vandene omsluttede mig indtil Sjælen, Dybet omgav mig, Tang var viklet om mit Hoved.
6 Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
Jeg sank ned til Bjergenes Grunde, Jordens Porte vare lukkede efter mig for evigt; men du Herre, min Gud, drog mit Liv op af Graven.
7 “Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
Der min Sjæl i mit Indre forsmægtede, kom jeg Herren i Hu; og min Bøn kom til dig i dit hellige Tempel.
8 “Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
De, som tage Vare paa Løgnens Gøglebilleder, de have forladt ham, som er dem Miskundhed.
9 Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
Men jeg, jeg vil med Taksigelses Røst ofre til dig, jeg vil betale det, jeg har lovet; Frelse er der hos Herren.
10 Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.
Og Herren bød Fisken, og den udspyede Jonas paa det tørre Land.

< Yunana 2 >