< Yunana 1 >
1 Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
HERRENs Ord kom til Jonas, Amittajs Søn, således:
2 “Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
"Stå op og gå til Nineve, den store Stad, udråb over den, at deres Ondskab er kommet op for mit Åsyn."
3 Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
Men Jonas stod op for at fly fra HERRENs Åsyn til Tarsis. Han drog ned til Jafo, og da han fandt et Skib, som skulde til Tarsis betalte han, hvad Rejsen kostede, og gik om Bord for at sejle med til Tarsis bort fra HERRENs Åsyn.
4 Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
Men HERREN Iod et stærkt Vejr fare hen over Havet, og en stærk Storm rejste sig på Havet, så Skibet var ved at gå under.
5 Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
Sømændene blev rædde og råbte hver til sin Gud, og de kastede alle Sager i Skibet over Bord for at lette det. Men Jonas var gået ned i det underste Skibsrum og lå i dyb Søvn dernede.
6 Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
Skibsføreren gik da ned til ham og sagde: "Hvor kan du sove? Stå op og råb til din Gud! Måske vil Gud komme os i Hu, så vi ikke omkommer."
7 Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
Så sagde de til hverandre: "Kom, lad os kaste Lod for at få at vide, hvem der er Skyld i, at denne Ulykke er tilstødt os!" Og de kastede Lod, og Loddet ramte Jonas.
8 Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
Da sagde de til ham: "Sig os, hvem der er Skyld i, at denne Ulykke er tilstødt os! Hvad er du, og hvor kommer du fra? Hvilket Land er du fra, og hvilket Folk hører du til?"
9 Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
Han svarede: "Jeg er Hebræer, og jeg frygter HERREN, Himmelens Gud, som har skabt Havet og det tørre Land."
10 Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
Så grebes Mændene af stor Rædsel og sagde til ham: "Hvad har du gjort!" Thi de fik at vide, at han flyede fra HERRENs Åsyn; det sagde han dem.
11 Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
Og de spurgte ham: "Hvad skal vi gøre med dig, så vi får Havet til at lægge sig? Thi det rejser sig mere og mere."
12 Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
Han svarede: "Tag og kast mig i Havet! Så får I det til at lægge sig; thi jeg ved, at jeg er Skyld i, at dette stærke Vejr er over eder."
13 Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
Mændene søgte nu at ro tilbage til Land, men kunde ikke, da Havet rejste sig mere og mere imod dem.
14 Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
Så råbte de til HERREN; "Ak, HERRE! Lad os ikke omkomme for denne Mands Sjæls Skyld og lad ikke uskyldigt Blod komme over os; thi det erjo dig, HERRE, derhar gjort, som du vilde."
15 Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
Derpå tog de Jonas og kastede ham i Havet, og straks lagde det sig.
16 Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
Og Mændene grebes af stor Rædsel for HERREN, bragte ham et Slagtoffer og aflagde Løfter.
17 Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.
Men HERREN bød en stor Fisk sluge Jonas; og Jonas var i Fiskens Bug tre Dage og tre Nætter.