< Yohanna 1 >

1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
Adau vAda AsIt sa cha vAda IshvareNa sArdhamAsIt sa vAdaH svayamIshvara eva|
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
sa AdAvIshvareNa sahAsIt|
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
tena sarvvaM vastu sasR^ije sarvveShu sR^iShTavastuShu kimapi vastu tenAsR^iShTaM nAsti|
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
sa jIvanasyAkAraH, tachcha jIvanaM manuShyANAM jyotiH
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
tajjyotirandhakAre prachakAshe kintvandhakArastanna jagrAha|
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
yohan nAmaka eko manuja IshvareNa preShayA nchakre|
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
tadvArA yathA sarvve vishvasanti tadarthaM sa tajjyotiShi pramANaM dAtuM sAkShisvarUpo bhUtvAgamat,
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
sa svayaM tajjyoti rna kintu tajjyotiShi pramANaM dAtumAgamat|
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
jagatyAgatya yaH sarvvamanujebhyo dIptiM dadAti tadeva satyajyotiH|
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
sa yajjagadasR^ijat tanmadya eva sa AsIt kintu jagato lokAstaM nAjAnan|
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
nijAdhikAraM sa AgachChat kintu prajAstaM nAgR^ihlan|
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
tathApi ye ye tamagR^ihlan arthAt tasya nAmni vyashvasan tebhya Ishvarasya putrA bhavitum adhikAram adadAt|
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
teShAM janiH shoNitAnna shArIrikAbhilAShAnna mAnavAnAmichChAto na kintvIshvarAdabhavat|
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
sa vAdo manuShyarUpeNAvatIryya satyatAnugrahAbhyAM paripUrNaH san sArdham asmAbhi rnyavasat tataH pituradvitIyaputrasya yogyo yo mahimA taM mahimAnaM tasyApashyAma|
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
tato yohanapi prachAryya sAkShyamidaM dattavAn yo mama pashchAd AgamiShyati sa matto gurutaraH; yato matpUrvvaM sa vidyamAna AsIt; yadartham ahaM sAkShyamidam adAM sa eShaH|
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
apara ncha tasya pUrNatAyA vayaM sarvve kramashaH kramashonugrahaM prAptAH|
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
mUsAdvArA vyavasthA dattA kintvanugrahaH satyatva ncha yIshukhrIShTadvArA samupAtiShThatAM|
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
kopi manuja IshvaraM kadApi nApashyat kintu pituH kroDastho. advitIyaH putrastaM prakAshayat|
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
tvaM kaH? iti vAkyaM preShTuM yadA yihUdIyalokA yAjakAn levilokAMshcha yirUshAlamo yohanaH samIpe preShayAmAsuH,
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
tadA sa svIkR^itavAn nApahnUtavAn nAham abhiShikta itya NgIkR^itavAn|
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
tadA te. apR^ichChan tarhi ko bhavAn? kiM eliyaH? sovadat na; tataste. apR^ichChan tarhi bhavAn sa bhaviShyadvAdI? sovadat nAhaM saH|
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
tadA te. apR^ichChan tarhi bhavAn kaH? vayaM gatvA prerakAn tvayi kiM vakShyAmaH? svasmin kiM vadasi?
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
tadA sovadat| parameshasya panthAnaM pariShkuruta sarvvataH| itIdaM prAntare vAkyaM vadataH kasyachidravaH| kathAmimAM yasmin yishayiyo bhaviShyadvAdI likhitavAn soham|
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
ye preShitAste phirUshilokAH|
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
tadA te. apR^ichChan yadi nAbhiShiktosi eliyosi na sa bhaviShyadvAdyapi nAsi cha, tarhi lokAn majjayasi kutaH?
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
tato yohan pratyavochat, toye. ahaM majjayAmIti satyaM kintu yaM yUyaM na jAnItha tAdR^isha eko jano yuShmAkaM madhya upatiShThati|
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
sa matpashchAd Agatopi matpUrvvaM varttamAna AsIt tasya pAdukAbandhanaM mochayitumapi nAhaM yogyosmi|
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
yarddananadyAH pArasthabaithabArAyAM yasminsthAne yohanamajjayat tasmina sthAne sarvvametad aghaTata|
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
pare. ahani yohan svanikaTamAgachChantaM yishuM vilokya prAvochat jagataH pApamochakam Ishvarasya meShashAvakaM pashyata|
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
yo mama pashchAdAgamiShyati sa matto gurutaraH, yato hetormatpUrvvaM so. avarttata yasminnahaM kathAmimAM kathitavAn sa evAyaM|
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
aparaM nAhamenaM pratyabhij nAtavAn kintu isrAyellokA enaM yathA parichinvanti tadabhiprAyeNAhaM jale majjayitumAgachCham|
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
punashcha yohanaparamekaM pramANaM datvA kathitavAn vihAyasaH kapotavad avatarantamAtmAnam asyoparyyavatiShThantaM cha dR^iShTavAnaham|
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
nAhamenaM pratyabhij nAtavAn iti satyaM kintu yo jale majjayituM mAM prairayat sa evemAM kathAmakathayat yasyoparyyAtmAnam avatarantam avatiShThanta ncha drakShayasi saeva pavitre Atmani majjayiShyati|
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
avastannirIkShyAyam Ishvarasya tanaya iti pramANaM dadAmi|
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
pare. ahani yohan dvAbhyAM shiShyAbhyAM sArddheM tiShThan
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
yishuM gachChantaM vilokya gaditavAn, Ishvarasya meShashAvakaM pashyataM|
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
imAM kathAM shrutvA dvau shiShyau yIshoH pashchAd IyatuH|
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
tato yIshuH parAvR^itya tau pashchAd AgachChantau dR^iShTvA pR^iShTavAn yuvAM kiM gaveshayathaH? tAvapR^ichChatAM he rabbi arthAt he guro bhavAn kutra tiShThati?
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
tataH sovAdit etya pashyataM| tato divasasya tR^itIyapraharasya gatatvAt tau taddinaM tasya sa Nge. asthAtAM|
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
yau dvau yohano vAkyaM shrutvA yishoH pashchAd AgamatAM tayoH shimonpitarasya bhrAtA AndriyaH
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
sa itvA prathamaM nijasodaraM shimonaM sAkShAtprApya kathitavAn vayaM khrIShTam arthAt abhiShiktapuruShaM sAkShAtkR^itavantaH|
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
pashchAt sa taM yishoH samIpam Anayat| tadA yIshustaM dR^iShTvAvadat tvaM yUnasaH putraH shimon kintu tvannAmadheyaM kaiphAH vA pitaraH arthAt prastaro bhaviShyati|
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
pare. ahani yIshau gAlIlaM gantuM nishchitachetasi sati philipanAmAnaM janaM sAkShAtprApyAvochat mama pashchAd AgachCha|
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
baitsaidAnAmni yasmin grAme pitarAndriyayorvAsa AsIt tasmin grAme tasya philipasya vasatirAsIt|
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
pashchAt philipo nithanelaM sAkShAtprApyAvadat mUsA vyavasthA granthe bhaviShyadvAdinAM grantheShu cha yasyAkhyAnaM likhitamAste taM yUShaphaH putraM nAsaratIyaM yIshuM sAkShAd akArShma vayaM|
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
tadA nithanel kathitavAn nAsarannagarAta kiM kashchiduttama utpantuM shaknoti? tataH philipo. avochat etya pashya|
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
apara ncha yIshuH svasya samIpaM tam AgachChantaM dR^iShTvA vyAhR^itavAn, pashyAyaM niShkapaTaH satya isrAyellokaH|
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
tataH sovadad, bhavAn mAM kathaM pratyabhijAnAti? yIshuravAdIt philipasya AhvAnAt pUrvvaM yadA tvamuDumbarasya tarormUle. asthAstadA tvAmadarsham|
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
nithanel achakathat, he guro bhavAn nitAntam Ishvarasya putrosi, bhavAn isrAyelvaMshasya rAjA|
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
tato yIshu rvyAharat, tvAmuDumbarasya pAdapasya mUle dR^iShTavAnAhaM mamaitasmAdvAkyAt kiM tvaM vyashvasIH? etasmAdapyAshcharyyANi kAryyANi drakShyasi|
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
anyachchAvAdId yuShmAnahaM yathArthaM vadAmi, itaH paraM mochite meghadvAre tasmAnmanujasUnunA Ishvarasya dUtagaNam avarohantamArohanta ncha drakShyatha|

< Yohanna 1 >