< Yohanna 1 >
1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
The same was in the beginning with God.
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
All things were made by him; and without him was not anything made that hath been made.
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
In him was life; and the life was the light of men.
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shineth in the darkness; and the darkness apprehended it not.
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
There came a man, sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
The same came for witness, that he might bear witness of the light, that all might believe through him.
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
He was not the light, but [came] that he might bear witness of the light.
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
There was the true light, [even the light] which lighteth every man, coming into the world.
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
He was in the world, and the world was made by him, and the world knew him not.
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
He came unto his own, and they that were his own received him not.
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
But as many as received him, to them gave he the right to become children of God, [even] to them that believe on his name:
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
which were born, not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
And the Word became flesh, and dwelt among us (and we beheld his glory, glory as of the only begotten from the Father), full of grace and truth.
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
John beareth witness of him, and crieth, saying, This was he of whom I said, He that cometh after me is become before me: for he was before me.
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
For of his fulness we all received, and grace for grace.
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
For the law was given by Moses; grace and truth came by Jesus Christ.
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
No man hath seen God at any time; the only begotten Son, which is in the bosom of the Father, he hath declared [him].
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
And this is the witness of John, when the Jews sent unto him from Jerusalem priests and Levites to ask him, Who art thou?
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
And he confessed, and denied not; and he confessed, I am not the Christ.
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
And they asked him, What then? Art thou Elijah? And he saith, I am not. Art thou the prophet? And he answered, No.
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
They said therefore unto him, Who art thou? that we may give an answer to them that sent us. What sayest thou of thyself?
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
He said, I am the voice of one crying in the wilderness, Make straight the way of the Lord, as said Isaiah the prophet.
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
And they had been sent from the Pharisees.
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
And they asked him, and said unto him, Why then baptizest thou, if thou art not the Christ, neither Elijah, neither the prophet?
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
John answered them, saying, I baptize with water: in the midst of you standeth one whom ye know not,
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
[even] he that cometh after me, the latchet of whose shoe I am not worthy to unloose.
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
These things were done in Bethany beyond Jordan, where John was baptizing.
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
On the morrow he seeth Jesus coming unto him, and saith, Behold, the Lamb of God, which taketh away the sin of the world!
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
This is he of whom I said, After me cometh a man which is become before me: for he was before me.
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
And I knew him not; but that he should be made manifest to Israel, for this cause came I baptizing with water.
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
And John bare witness, saying, I have beheld the Spirit descending as a dove out of heaven; and it abode upon him.
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
And I knew him not: but he that sent me to baptize with water, he said unto me, Upon whomsoever thou shalt see the Spirit descending, and abiding upon him, the same is he that baptizeth with the Holy Spirit.
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
And I have seen, and have borne witness that this is the Son of God.
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
Again on the morrow John was standing, and two of his disciples;
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
and he looked upon Jesus as he walked, and saith, Behold, the Lamb of God!
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
And the two disciples heard him speak, and they followed Jesus.
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
And Jesus turned, and beheld them following, and saith unto them, What seek ye? And they said unto him, Rabbi (which is to say, being interpreted, Master), where abidest thou?
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
He saith unto them, Come, and ye shall see. They came therefore and saw where he abode; and they abode with him that day: it was about the tenth hour.
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
One of the two that heard John [speak], and followed him, was Andrew, Simon Peter’s brother.
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
He findeth first his own brother Simon, and saith unto him, We have found the Messiah (which is, being interpreted, Christ).
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
He brought him unto Jesus. Jesus looked upon him, and said, Thou art Simon the son of John: thou shalt be called Cephas (which is by interpretation, Peter).
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
On the morrow he was minded to go forth into Galilee, and he findeth Philip: and Jesus saith unto him, Follow me.
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
Now Philip was from Bethsaida, of the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
Philip findeth Nathanael, and saith unto him, We have found him, of whom Moses in the law, and the prophets, did write, Jesus of Nazareth, the son of Joseph.
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
And Nathanael said unto him, Can any good thing come out of Nazareth? Philip saith unto him, Come and see.
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
Jesus saw Nathanael coming to him, and saith of him, Behold, an Israelite indeed, in whom is no guile!
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
Nathanael saith unto him, Whence knowest thou me? Jesus answered and said unto him, Before Philip called thee, when thou wast under the fig tree, I saw thee.
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
Nathanael answered him, Rabbi, thou art the Son of God; thou art King of Israel.
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
Jesus answered and said unto him, Because I said unto thee, I saw thee underneath the fig tree, believest thou? thou shalt see greater things than these.
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
And he saith unto him, Verily, verily, I say unto you, Ye shall see the heaven opened, and the angels of God ascending and descending upon the Son of man.