< Yohanna 9 >
1 Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
Et comme il passait, Jésus vit un homme aveugle de naissance;
2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
Et ses disciples l’interrogèrent: Maître, qui a péché, celui-ci ou ses parents, pour qu’il soit né aveugle?
3 Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
Jésus répondit: Ni celui-ci n’a péché, ni ses parents, mais c’est pour que les œuvres de Dieu soient manifestées en lui.
4 Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
Il faut que j’opère les œuvres de celui qui m’a envoyé, tandis qu’il est jour; la nuit vient, pendant laquelle personne ne peut agir;
5 Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
Tant que je suis dans le monde, je suis la lumière du monde.
6 Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
Lorsqu’il eut dit cela, il cracha à terre, fit de la boue avec sa salive, et frotta de cette boue les yeux de l’aveugle,
7 Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
Et il lui dit: Va, lave-toi dans la piscine de Siloé (ce qu’on interprète par Envoyé). Il s’en alla donc, se lava, et revint voyant clair.
8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
De sorte que ses voisins et ceux qui l’avaient vu auparavant mendier, disaient: N’est-ce pas celui-là qui était assis et mendiait? D’autres disaient: c’est lui.
9 Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
Et d’autres: Point du tout, seulement il lui ressemble. Mais lui disait: C’est moi.
10 Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
Ils lui demandaient donc: Comment tes yeux ont-ils été ouverts?
11 Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
Il répondit: Cet homme qu’on appelle Jésus a fait de la boue, il a frotté mes yeux, et m’a dit: Va à la piscine de Siloé, et lave-toi. J’y suis allé, je me suis lavé, et je vois.
12 Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
Ils lui demandèrent: Où est-il? Il répondit: Je ne sais.
13 Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
Alors ils amenèrent aux pharisiens celui qui avait été aveugle.
14 To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
Or c’était un jour de sabbat que Jésus fit de la boue et ouvrit ses yeux.
15 Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
Les pharisiens lui demandèrent donc aussi comment il avait vu. Et il leur dit: Il m’a mis de la boue sur les yeux, je me suis lavé, et je vois.
16 Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
Alors quelques-uns d’entre les pharisiens disaient: Cet homme n’est point de Dieu, puisqu’il ne garde point le sabbat. Mais d’autres disaient: Comment un pécheur peut-il faire de tels miracles? Et il y avait division entre eux.
17 A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
Ils dirent donc encore à l’aveugle: Et toi, que dis-tu de celui qui t’a ouvert les yeux? Il répondit: C’est un prophète.
18 Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
Mais les Juifs ne crurent point de lui qu’il eût été aveugle et qu’il eût recouvré la vue, jusqu’à ce qu’ils eussent appelé les parents de celui qui avait recouvré la vue;
19 Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
Et ils les interrogèrent, disant: Est-ce là votre fils, que vous dites être né aveugle? Comment donc voit-il maintenant?
20 Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
Ses parents leur répondirent et dirent: Nous savons que c’est notre fils et qu’il est né aveugle;
21 Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
Mais comment il voit maintenant, nous ne le savons pas; ou qui lui a ouvert les yeux, nous ne le savons pas; interrogez-le: il a de l’âge, qu’il parle pour lui-même.
22 Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
Ses parents dirent cela, parce qu’ils craignaient les Juifs; car déjà les Juifs étaient convenus ensemble que si quelqu’un confessait que Jésus était le Christ, il serait chassé de la synagogue.
23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
C’est pourquoi ses parents dirent: Il a de l’âge, interrogez-le lui-même.
24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
Ils appelèrent donc de nouveau l’homme qui avait été aveugle, et lui dirent: Rends gloire à Dieu; pour nous, nous savons que cet homme est un pécheur.
25 Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
Mais il leur dit: S’il est pécheur, je ne sais; je sais une seule chose, c’est que j’étais aveugle, et qu’à présent je vois.
26 Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
Ils lui répliquèrent donc: Que t’a-t-il fait? Comment t’a-t-il ouvert les yeux?
27 Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
Il leur répondit: Je vous l’ai déjà dit, et vous l’avez entendu, pourquoi voulez-vous l’entendre encore? Est-ce que, vous aussi, vous voulez devenir ses disciples?
28 Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
Ils le maudirent donc, et dirent: Sois son disciple, toi; mais nous, nous sommes disciples de Moïse.
29 Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
Nous savons que Dieu a parlé à Moïse; mais celui-ci, nous ne savons d’où il est.
30 Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
Cet homme reprit et leur dit: Mais il y a en cela une chose étonnante, c’est que vous ne sachiez d’où il est, et il a ouvert mes yeux;
31 Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
Cependant nous savons que Dieu n’écoute point les pécheurs; mais si quelqu’un honore Dieu et fait sa volonté, c’est celui-là qu’il exauce.
32 Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn )
Jamais on n’a ouï dire que quelqu’un ait ouvert les yeux d’un aveugle-né. (aiōn )
33 Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
Si celui-ci n’était pas de Dieu, il ne pourrait rien faire.
34 Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
Ils répliquèrent et lui dirent: Tu es né tout entier dans le péché, et tu nous enseignes! Et ils le jetèrent dehors.
35 Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
Jésus apprit qu’ils l’avaient jeté dehors; et, l’ayant rencontré, il lui demanda: Crois-tu au Fils de Dieu?
36 Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
Celui-ci répondit et dit: Qui est-il, Seigneur, afin que je croie en lui?
37 Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
Et Jésus lui dit: Mais tu l’as vu, et c’est lui-même qui te parle.
38 Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
Et celui-ci reprit: Je crois. Seigneur; et se prosternant, il l’adora.
39 Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
Alors Jésus dit: C’est en jugement que je suis venu dans ce monde, afin que ceux qui ne voient pas, voient, et que ceux qui voient, deviennent aveugles.
40 Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
Or quelques-uns d’entre les pharisiens, qui étaient avec lui, l’entendirent et lui demandèrent: Est-ce que nous sommes aveugles, nous aussi?
41 Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.
Jésus leur répondit: Si vous étiez aveugles, vous n’auriez point de péché. Mais vous dites au contraire: Nous voyons. Ainsi votre péché subsiste.