< Yohanna 9 >

1 Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
As He passed by, He saw a man who had been blind from his birth.
2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
So His disciples asked Him, "Rabbi, who sinned--this man or his parents--that he was born blind?"
3 Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
"Neither he nor his parents sinned," answered Jesus, "but he was born blind in order that God's mercy might be openly shown in him.
4 Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
We must do the works of Him who sent me while there is daylight. Night is coming on, when no one can work.
5 Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
When I am in the world, I am the Light of the world."
6 Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
After thus speaking, He spat on the ground, and then, kneading the dust and spittle into clay, He smeared the clay over the man's eyes and said to him,
7 Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
"Go and wash in the pool of Siloam" --the name means 'Sent.' So he went and washed his eyes, and returned able to see.
8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
His neighbours, therefore, and the other people to whom he had been a familiar object because he was a beggar, began asking, "Is not this the man who used to sit and beg?"
9 Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
"Yes it is," replied some of them. "No it is not," said others, "but he is like him." His own statement was, "I am the man."
10 Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
"How then were your eyes opened?" they asked.
11 Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
"He whose name is Jesus," he answered, "made clay and smeared my eyes with it, and then told me to go to Siloam and wash. So I went and washed and obtained sight."
12 Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
"Where is he?" they inquired, but the man did not know.
13 Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
They brought him to the Pharisees--the man who had been blind.
14 To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
Now the day on which Jesus made the clay and opened the man's eyes was the Sabbath.
15 Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
So the Pharisees renewed their questioning as to how he had obtained his sight. "He put clay on my eyes," he replied, "and I washed, and now I can see."
16 Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
This led some of the Pharisees to say, "That man has not come from God, for he does not keep the Sabbath." "How is it possible for a bad man to do such miracles?" argued others.
17 A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
And there was a division among them. So again they asked the once blind man, "What is your account of him? --for he opened your eyes." "He is a Prophet," he replied.
18 Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
The Jews, however, did not believe the statement concerning him--that he had been blind and had obtained his sight--until they called his parents and asked them,
19 Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
"Is this your son, who you say was born blind? How is it then that he can now see?"
20 Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
"We know," replied the parents, "that this is our son and that he was born blind;
21 Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
but how it is that he can now see or who has opened his eyes we do not know. Ask him himself; he is of full age; he himself will give his own account of it."
22 Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
Such was their answer, because they were afraid of the Jews; for the Jews had already settled among themselves that if any one should acknowledge Jesus as the Christ, he should be excluded from the synagogue.
23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
That was why his parents said, "He is of full age: ask him himself."
24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
A second time therefore they called the man who had been blind, and said, "Give God the praise: we know that that man is a sinner."
25 Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
"Whether he is a sinner or not, I do not know," he replied; "one thing I know--that I was once blind and that now I can see."
26 Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
"What did he do to you?" they asked; "how did he open your eyes?"
27 Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
"I have told you already," he replied, "and you did not listen to me. Why do you want to hear it again? Do you also mean to be disciples of his?"
28 Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
Then they railed at him, and said, "You are that man's disciple, but we are disciples of Moses.
29 Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
We know that God spoke to Moses; but as for this fellow we do not know where he comes from."
30 Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
"Why, this is marvellous!" the man replied; "you do not know where he comes from, and yet he has opened my eyes!
31 Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
We know that God does not listen to bad people, but that if any one is a God-fearing man and obeys Him, to him He listens.
32 Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn g165)
From the beginning of the world such a thing was never heard of as that any one should open the eyes of a man blind from his birth. (aiōn g165)
33 Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
Had that man not come from God, he could have done nothing."
34 Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
"You," they replied, "were wholly begotten and born in sin, and do you teach us?" And they put him out of the synagogue.
35 Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
Jesus heard that they had done this. So having found him, He asked him, "Do you believe in the Son of God?"
36 Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
"Who is He, Sir?" replied the man. "Tell me, so that I may believe in Him."
37 Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
"You have seen Him," said Jesus; "and not only so: He is now speaking to you."
38 Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
"I believe, Sir," he said. And he threw himself at His feet.
39 Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
"I came into this world," said Jesus, "to judge men, that those who do not see may see, and that those who do see may become blind."
40 Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
These words were heard by those of the Pharisees who were present, and they asked Him, "Are we also blind?"
41 Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.
"If you were blind," answered Jesus, "you would have no sin; but as a matter of fact you boast that you see. So your sin remains!"

< Yohanna 9 >