< Yohanna 9 >
1 Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
And as Jesus passed by, he saw a man which was blind from his birth.
2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
And his disciples asked him, saying, Master, who did sin, this man, or his parents, that he was born blind?
3 Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
Jesus answered, Neither has this man sinned, nor his parents: but that the works of God should be made manifest in him.
4 Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
I must work the works of him that sent me, while it is day: the night comes, when no man can work.
5 Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
As long as I am in the world, I am the light of the world.
6 Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
When he had thus spoken, he spat on the ground, and made clay of the spittle, and he anointed the eyes of the blind man with the clay,
7 Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
And said unto him, Go, wash in the pool of Siloam, (which is by interpretation, Sent.) He went his way therefore, and washed, and came seeing.
8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
The neighbours therefore, and they which before had seen him that he was blind, said, Is not this he that sat and begged?
9 Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
Some said, This is he: others said, He is like him: but he said, I am he.
10 Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
Therefore said they unto him, How were your eyes opened?
11 Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
He answered and said, A man that is called Jesus made clay, and anointed mine eyes, and said unto me, Go to the pool of Siloam, and wash: and I went and washed, and I received sight.
12 Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
Then said they unto him, Where is he? He said, I know not.
13 Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
They brought to the Pharisees him that in old times was blind.
14 To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
And it was the sabbath day when Jesus made the clay, and opened his eyes.
15 Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
Then again the Pharisees also asked him how he had received his sight. He said unto them, He put clay upon mine eyes, and I washed, and do see.
16 Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
Therefore said some of the Pharisees, This man is not of God, because he keeps not the sabbath day. Others said, How can a man that is a sinner do such miracles? And there was a division among them.
17 A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
They say unto the blind man again, What say you of him, that he has opened your eyes? He said, He is a prophet.
18 Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
But the Jews did not believe concerning him, that he had been blind, and received his sight, until they called the parents of him that had received his sight.
19 Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
And they asked them, saying, Is this your son, who all of you say was born blind? how then does he now see?
20 Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
His parents answered them and said, We know that this is our son, and that he was born blind:
21 Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
But by what means he now sees, we know not; or who has opened his eyes, we know not: he is of age; ask him: he shall speak for himself.
22 Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
These words spoke his parents, because they feared the Jews: for the Jews had agreed already, that if any man did confess that he was Christ, he should be put out of the synagogue.
23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
Therefore said his parents, He is of age; ask him.
24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
Then again called they the man that was blind, and said unto him, Give God the praise: we know that this man is a sinner.
25 Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
He answered and said, Whether he be a sinner or no, I know not: one thing I know, that, whereas I was blind, now I see.
26 Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
Then said they to him again, What did he to you? how opened he your eyes?
27 Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
He answered them, I have told you already, and all of you did not hear: wherefore would all of you hear it again? will all of you also be his disciples?
28 Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
Then they reviled him, and said, You are his disciple; but we are Moses' disciples.
29 Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
We know that God spoke unto Moses: as for this fellow, we know not from whence he is.
30 Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
The man answered and said unto them, Why herein is a marvellous thing, that all of you know not from whence he is, and yet he has opened mine eyes.
31 Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
Now we know that God hears not sinners: but if any man be a worshipper of God, and does his will, him he hears.
32 Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn )
Since the world began was it not heard that any man opened the eyes of one that was born blind. (aiōn )
33 Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
If this man were not of God, he could do nothing.
34 Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
They answered and said unto him, You were altogether born in sins, and do you teach us? And they cast him out.
35 Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
Jesus heard that they had cast him out; and when he had found him, he said unto him, Do you believe on the Son of God?
36 Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
He answered and said, Who is he, Lord, that I might believe on him?
37 Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
And Jesus said unto him, You have both seen him, and it is he that talks with you.
38 Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
And he said, Lord, I believe. And he worshipped him.
39 Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
And Jesus said, For judgment I am come into this world, that they which see not might see; and that they which see might be made blind.
40 Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
And some of the Pharisees which were with him heard these words, and said unto him, Are we blind also?
41 Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.
Jesus said unto them, If all of you were blind, all of you should have no sin: but now all of you say, We see; therefore your sin remains.