< Yohanna 9 >
1 Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
Now as He was passing by He saw a man blind from birth.
2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
And His disciples asked Him saying, “Rabbi, who sinned, this man or his parents, in that he was born blind?”
3 Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
Jesus answered: “Neither this man nor his parents sinned, but so that the works of God might be displayed in him.
4 Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
I must accomplish the works of Him who sent me while it is day; night is coming when no one can work.
5 Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
While I am in the world, I am the Light of the world.”
6 Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
Upon saying these things He spat on the ground and made mud with the saliva, and spread the mud on the blind man's eyes.
7 Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
And He said to him, “Go wash in the pool of Siloam” (which is translated, ‘Sent’). So he went and washed, and came away seeing!
8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
Then the neighbors and those who previously had seen that he was blind started saying, “Isn't this the man who sat begging?”
9 Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
Others said, “This is he”; still others, “He is like him.” He kept saying, “I'm the one!”
10 Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
So they said to him, “How were your eyes opened?”
11 Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
He answered and said: “A man called Jesus made mud and anointed my eyes and said to me, ‘Go to the pool of Siloam and wash.’ So when I went and washed, I saw!”
12 Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
Then they said to him, “Where is He?” He says, “I don't know.”
13 Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
They bring the man who was formerly blind to the Pharisees.
14 To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
(Now it was a Sabbath when Jesus made the mud and opened his eyes.)
15 Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
So once again the Pharisees also asked him how he had received his sight. So he said to them, “He put mud on my eyes, and I washed, and I see.”
16 Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
Then some of the Pharisees said, “This man cannot be from God, because he does not keep the Sabbath,” Others were saying, “How can a sinful man do such signs?” And there was a division among them.
17 A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
So they address the blind man again, “What do you say about him, in that he opened your eyes?” He said, “He is a prophet.”
18 Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
However the Jews did not believe concerning him that he was blind and received sight until they summoned the parents of the one who had received sight.
19 Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
And they asked them saying: “Is this your son, whom you say was born blind? How then does he now see?”
20 Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
So his parents answered them and said: “We know that this is our son, and that he was born blind;
21 Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
but by what means he now sees we don't know, or who opened his eyes we don't know. He is of age. Ask him. He will speak for himself.”
22 Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
His parents said these things because they feared the Jews, because the Jews had already agreed that if anyone confessed Him to be Christ he would be barred from the synagogue.
23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
That is why his parents said, “He is of age; ask him.”
24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
So they summoned the man who had been blind a second time and said to him: “Give glory to God! We know that this man is a sinner.”
25 Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
So he answered and said: “That He is a sinner, I do not know. One thing I do know, that having been blind I now see!”
26 Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
So they said to him again: “What did he do to you? How did he open your eyes?”
27 Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
He answered them: “I already told you and you didn't listen. Why do you want to hear it again? You don't want to become His disciples too, do you?”
28 Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
They reviled him and said: “You are that fellow's disciple, but we are Moses' disciples.
29 Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
We know that God spoke to Moses; but this fellow—we don't know where he's from.”
30 Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
The man answered and said to them: “Why, this is remarkable—you don't know where He is from; yet He opened my eyes!
31 Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
Now we know that God doesn't listen to sinners; but if anyone is God-fearing and does His will, to him He listens.
32 Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn )
Since time began it was never heard that anyone opened the eyes of a person born blind. (aiōn )
33 Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
If this man were not from God he would not be able to do anything.”
34 Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
They answered and said to him, “You were totally born in sins, and you are teaching us?” And they expelled him.
35 Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
Jesus heard that they had expelled him, and finding him He said to him, “Do you believe into the Son of God?”
36 Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
He answered and said, “And who is He, Lord, that I may believe into Him?”
37 Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
So Jesus said to him, “You have both seen Him and He is the One who is speaking with you.”
38 Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
So he said, “Lord, I believe!” And he worshiped Him.
39 Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
And Jesus said, “I came into this world for judgment, so that those who do not see may see, and those who ‘see’ may become blind.”
40 Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
And some of the Pharisees who were with Him heard these words and said to Him, “We aren't blind too, are we?”
41 Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.
Jesus said to them: “If you were ‘blind’ you would not have sin. But now you say, ‘We see,’ so your sin remains.