< Yohanna 9 >
1 Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
Now as Jesus was passing by, He saw a man blind from birth,
2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
and His disciples asked Him, “Rabbi, who sinned, this man or his parents, that he was born blind?”
3 Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
Jesus answered, “Neither this man nor his parents sinned, but this happened so that the works of God would be displayed in him.
4 Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
While it is daytime, we must do the works of Him who sent Me. Night is coming, when no one can work.
5 Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
While I am in the world, I am the light of the world.”
6 Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
When Jesus had said this, He spit on the ground, made some mud, and applied it to the man’s eyes.
7 Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
Then He told him, “Go, wash in the Pool of Siloam” (which means “Sent”). So the man went and washed, and came back seeing.
8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
At this, his neighbors and those who had formerly seen him begging began to ask, “Isn’t this the man who used to sit and beg?”
9 Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
Some claimed that he was, but others said, “No, he just looks like him.” But the man kept saying, “I am the one.”
10 Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
“How then were your eyes opened?” they asked.
11 Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
He answered, “The man they call Jesus made some mud and anointed my eyes, and He told me to go to Siloam and wash. So I went and washed and received my sight.”
12 Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
“Where is He?” they asked. “I do not know,” he answered.
13 Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
They brought to the Pharisees the man who had been blind.
14 To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
Now the day on which Jesus had made the mud and opened his eyes was a Sabbath.
15 Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
So the Pharisees also asked him how he had received his sight. The man answered, “He put mud on my eyes, and I washed, and now I can see.”
16 Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
Because of this, some of the Pharisees said, “This man is not from God, for He does not keep the Sabbath.” But others said, “How can a sinful man perform such signs?” And there was division among them.
17 A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
So once again they asked the man who had been blind, “What do you say about Him, since it was your eyes He opened?” “He is a prophet,” the man replied.
18 Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
The Jews still did not believe that the man had been blind and had received his sight until they summoned his parents
19 Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
and asked, “Is this your son, the one you say was born blind? So how is it that he can now see?”
20 Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
His parents answered, “We know he is our son, and we know he was born blind.
21 Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
But how he can now see or who opened his eyes, we do not know. Ask him. He is old enough to speak for himself.”
22 Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
His parents said this because they were afraid of the Jews. For the Jews had already determined that anyone who confessed Jesus as the Christ would be put out of the synagogue.
23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
That was why his parents said, “He is old enough. Ask him.”
24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
So a second time they called for the man who had been blind and said, “Give glory to God! We know that this man is a sinner.”
25 Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
He answered, “Whether He is a sinner I do not know. There is one thing I do know: I was blind, but now I see!”
26 Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
“What did He do to you?” they asked. “How did He open your eyes?”
27 Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
He replied, “I already told you, and you did not listen. Why do you want to hear it again? Do you also want to become His disciples?”
28 Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
Then they heaped insults on him and said, “You are His disciple; we are disciples of Moses.
29 Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
We know that God spoke to Moses, but we do not know where this man is from.”
30 Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
“That is remarkable indeed!” the man said. “You do not know where He is from, and yet He opened my eyes.
31 Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
We know that God does not listen to sinners, but He does listen to the one who worships Him and does His will.
32 Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn )
Never before has anyone heard of opening the eyes of a man born blind. (aiōn )
33 Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
If this man were not from God, He could do no such thing.”
34 Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
They replied, “You were born in utter sin, and you are instructing us?” And they threw him out.
35 Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
When Jesus heard that they had thrown him out, He found the man and said, “Do you believe in the Son of Man?”
36 Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
“Who is He, Sir?” he replied. “Tell me so that I may believe in Him.”
37 Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
“You have already seen Him,” Jesus answered. “He is the One speaking with you.”
38 Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
“Lord, I believe,” he said. And he worshiped Jesus.
39 Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
Then Jesus declared, “For judgment I have come into this world, so that the blind may see and those who see may become blind.”
40 Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
Some of the Pharisees who were with Him heard this, and they asked Him, “Are we blind too?”
41 Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.
“If you were blind,” Jesus replied, “you would not be guilty of sin. But since you claim you can see, your guilt remains.”