< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
pratyUShe yIshuH panarmandiram AgachChat
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
tataH sarvveShu lokeShu tasya samIpa AgateShu sa upavishya tAn upadeShTum Arabhata|
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
tadA adhyApakAH phirUshina ncha vyabhichArakarmmaNi dhR^itaM striyamekAm Aniya sarvveShAM madhye sthApayitvA vyAharan
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
he guro yoShitam imAM vyabhichArakarmma kurvvANAM lokA dhR^itavantaH|
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
etAdR^ishalokAH pAShANAghAtena hantavyA iti vidhirmUsAvyavasthAgranthe likhitosti kintu bhavAn kimAdishati?
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
te tamapavadituM parIkShAbhiprAyeNa vAkyamidam apR^ichChan kintu sa prahvIbhUya bhUmAva NgalyA lekhitum Arabhata|
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
tatastaiH punaH punaH pR^iShTa utthAya kathitavAn yuShmAkaM madhye yo jano niraparAdhI saeva prathamam enAM pAShANenAhantu|
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
pashchAt sa punashcha prahvIbhUya bhUmau lekhitum Arabhata|
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
tAM kathaM shrutvA te svasvamanasi prabodhaM prApya jyeShThAnukramaM ekaikashaH sarvve bahiragachChan tato yIshurekAkI tayakttobhavat madhyasthAne daNDAyamAnA sA yoShA cha sthitA|
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
tatpashchAd yIshurutthAya tAM vanitAM vinA kamapyaparaM na vilokya pR^iShTavAn he vAme tavApavAdakAH kutra? kopi tvAM kiM na daNDayati?
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
sAvadat he mahechCha kopi na tadA yIshuravochat nAhamapi daNDayAmi yAhi punaH pApaM mAkArShIH|
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
tato yIshuH punarapi lokebhya itthaM kathayitum Arabhata jagatohaM jyotiHsvarUpo yaH kashchin matpashchAda gachChati sa timire na bhramitvA jIvanarUpAM dIptiM prApsyati|
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
tataH phirUshino. avAdiShustvaM svArthe svayaM sAkShyaM dadAsi tasmAt tava sAkShyaM grAhyaM na bhavati|
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
tadA yIshuH pratyuditavAn yadyapi svArthe. ahaM svayaM sAkShyaM dadAmi tathApi mat sAkShyaM grAhyaM yasmAd ahaM kuta Agatosmi kva yAmi cha tadahaM jAnAmi kintu kuta Agatosmi kutra gachChAmi cha tad yUyaM na jAnItha|
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
yUyaM laukikaM vichArayatha nAhaM kimapi vichArayAmi|
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
kintu yadi vichArayAmi tarhi mama vichAro grahItavyo yatoham ekAkI nAsmi prerayitA pitA mayA saha vidyate|
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
dvayo rjanayoH sAkShyaM grahaNIyaM bhavatIti yuShmAkaM vyavasthAgranthe likhitamasti|
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
ahaM svArthe svayaM sAkShitvaM dadAmi yashcha mama tAto mAM preritavAn sopi madarthe sAkShyaM dadAti|
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
tadA te. apR^ichChan tava tAtaH kutra? tato yIshuH pratyavAdId yUyaM mAM na jAnItha matpitara ncha na jAnItha yadi mAm akShAsyata tarhi mama tAtamapyakShAsyata|
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
yIshu rmandira upadishya bhaNDAgAre kathA etA akathayat tathApi taM prati kopi karaM nodatolayat|
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
tataH paraM yIshuH punaruditavAn adhunAhaM gachChAmi yUyaM mAM gaveShayiShyatha kintu nijaiH pApai rmariShyatha yat sthAnam ahaM yAsyAmi tat sthAnam yUyaM yAtuM na shakShyatha|
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
tadA yihUdIyAH prAvochan kimayam AtmaghAtaM kariShyati? yato yat sthAnam ahaM yAsyAmi tat sthAnam yUyaM yAtuM na shakShyatha iti vAkyaM bravIti|
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
tato yIshustebhyaH kathitavAn yUyam adhaHsthAnIyA lokA aham UrdvvasthAnIyaH yUyam etajjagatsambandhIyA aham etajjagatsambandhIyo na|
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
tasmAt kathitavAn yUyaM nijaiH pApai rmariShyatha yatohaM sa pumAn iti yadi na vishvasitha tarhi nijaiH pApai rmariShyatha|
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
tadA te. apR^ichChan kastvaM? tato yIshuH kathitavAn yuShmAkaM sannidhau yasya prastAvam A prathamAt karomi saeva puruShohaM|
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
yuShmAsu mayA bahuvAkyaM vakttavyaM vichArayitavya ncha kintu matprerayitA satyavAdI tasya samIpe yadahaM shrutavAn tadeva jagate kathayAmi|
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
kintu sa janake vAkyamidaM prokttavAn iti te nAbudhyanta|
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
tato yIshurakathayad yadA manuShyaputram Urdvva utthApayiShyatha tadAhaM sa pumAn kevalaH svayaM kimapi karmma na karomi kintu tAto yathA shikShayati tadanusAreNa vAkyamidaM vadAmIti cha yUyaM j nAtuM shakShyatha|
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
matprerayitA pitA mAm ekAkinaM na tyajati sa mayA sArddhaM tiShThati yatohaM tadabhimataM karmma sadA karomi|
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
tadA tasyaitAni vAkyAni shrutvA bahuvastAsmin vyashvasan|
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
ye yihUdIyA vyashvasan yIshustebhyo. akathayat
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
mama vAkye yadi yUyam AsthAM kurutha tarhi mama shiShyA bhUtvA satyatvaM j nAsyatha tataH satyatayA yuShmAkaM mokSho bhaviShyati|
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
tadA te pratyavAdiShuH vayam ibrAhImo vaMshaH kadApi kasyApi dAsA na jAtAstarhi yuShmAkaM muktti rbhaviShyatIti vAkyaM kathaM bravIShi?
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
tadA yIshuH pratyavadad yuShmAnahaM yathArthataraM vadAmi yaH pApaM karoti sa pApasya dAsaH|
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
dAsashcha nirantaraM niveshane na tiShThati kintu putro nirantaraM tiShThati| (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
ataH putro yadi yuShmAn mochayati tarhi nitAntameva mukttA bhaviShyatha|
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
yuyam ibrAhImo vaMsha ityahaM jAnAmi kintu mama kathA yuShmAkam antaHkaraNeShu sthAnaM na prApnuvanti tasmAddheto rmAM hantum Ihadhve|
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
ahaM svapituH samIpe yadapashyaM tadeva kathayAmi tathA yUyamapi svapituH samIpe yadapashyata tadeva kurudhve|
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
tadA te pratyavochan ibrAhIm asmAkaM pitA tato yIshurakathayad yadi yUyam ibrAhImaH santAnA abhaviShyata tarhi ibrAhIma AchAraNavad AchariShyata|
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
Ishvarasya mukhAt satyaM vAkyaM shrutvA yuShmAn j nApayAmi yohaM taM mAM hantuM cheShTadhve ibrAhIm etAdR^ishaM karmma na chakAra|
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
yUyaM svasvapituH karmmANi kurutha tadA tairukttaM na vayaM jArajAtA asmAkam ekaeva pitAsti sa eveshvaraH
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
tato yIshunA kathitam Ishvaro yadi yuShmAkaM tAtobhaviShyat tarhi yUyaM mayi premAkariShyata yatoham IshvarAnnirgatyAgatosmi svato nAgatohaM sa mAM prAhiNot|
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
yUyaM mama vAkyamidaM na budhyadhve kutaH? yato yUyaM mamopadeshaM soDhuM na shaknutha|
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
yUyaM shaitAn pituH santAnA etasmAd yuShmAkaM piturabhilAShaM pUrayatha sa A prathamAt naraghAtI tadantaH satyatvasya leshopi nAsti kAraNAdataH sa satyatAyAM nAtiShThat sa yadA mR^iShA kathayati tadA nijasvabhAvAnusAreNaiva kathayati yato sa mR^iShAbhAShI mR^iShotpAdakashcha|
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
ahaM tathyavAkyaM vadAmi kAraNAdasmAd yUyaM mAM na pratItha|
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
mayi pApamastIti pramANaM yuShmAkaM ko dAtuM shaknoti? yadyahaM tathyavAkyaM vadAmi tarhi kuto mAM na pratitha?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
yaH kashchana IshvarIyo lokaH sa IshvarIyakathAyAM mano nidhatte yUyam IshvarIyalokA na bhavatha tannidAnAt tatra na manAMsi nidhadve|
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
tadA yihUdIyAH pratyavAdiShuH tvamekaH shomiroNIyo bhUtagrastashcha vayaM kimidaM bhadraM nAvAdiShma?
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
tato yIshuH pratyavAdIt nAhaM bhUtagrastaH kintu nijatAtaM sammanye tasmAd yUyaM mAm apamanyadhve|
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
ahaM svasukhyAtiM na cheShTe kintu cheShTitA vichArayitA chApara eka Aste|
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
ahaM yuShmabhyam atIva yathArthaM kathayAmi yo naro madIyaM vAchaM manyate sa kadAchana nidhanaM na drakShyati| (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
yihUdIyAstamavadan tvaM bhUtagrasta itIdAnIm avaiShma| ibrAhIm bhaviShyadvAdina ncha sarvve mR^itAH kintu tvaM bhAShase yo naro mama bhAratIM gR^ihlAti sa jAtu nidhAnAsvAdaM na lapsyate| (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
tarhi tvaM kim asmAkaM pUrvvapuruShAd ibrAhImopi mahAn? yasmAt sopi mR^itaH bhaviShyadvAdinopi mR^itAH tvaM svaM kaM pumAMsaM manuShe?
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
yIshuH pratyavochad yadyahaM svaM svayaM sammanye tarhi mama tat sammananaM kimapi na kintu mama tAto yaM yUyaM svIyam IshvaraM bhAShadhve saeva mAM sammanute|
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
yUyaM taM nAvagachChatha kintvahaM tamavagachChAmi taM nAvagachChAmIti vAkyaM yadi vadAmi tarhi yUyamiva mR^iShAbhAShI bhavAmi kintvahaM tamavagachChAmi tadAkShAmapi gR^ihlAmi|
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
yuShmAkaM pUrvvapuruSha ibrAhIm mama samayaM draShTum atIvAvA nChat tannirIkShyAnandachcha|
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
tadA yihUdIyA apR^ichChan tava vayaH pa nchAshadvatsarA na tvaM kim ibrAhImam adrAkShIH?
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
yIshuH pratyavAdId yuShmAnahaM yathArthataraM vadAmi ibrAhImo janmanaH pUrvvakAlamArabhyAhaM vidye|
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
tadA te pAShANAn uttolya tamAhantum udayachChan kintu yIshu rgupto mantirAd bahirgatya teShAM madhyena prasthitavAn|

< Yohanna 8 >