< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
Jésus s’en alla sur la montagne des Oliviers;
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
mais, dès le point du jour, il retourna dans le temple, et tout le peuple vint à lui. Et s’étant assis, il les enseignait.
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
Alors les Scribes et les Pharisiens lui amenèrent une femme surprise en adultère, et l’ayant fait avancer,
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
ils dirent à Jésus: « Maître, cette femme a été surprise en flagrant délit d’adultère.
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
Or Moïse, dans la Loi, nous a ordonné de lapider de telles personnes. Vous donc, que dites-vous? »
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
C’était pour l’éprouver qu’ils l’interrogeaient ainsi, afin de pouvoir l’accuser. Mais Jésus, s’étant baissé, écrivait sur la terre avec le doigt.
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
Comme ils continuaient à l’interroger, il se releva et leur dit: « Que celui de vous qui est sans péché lui jette la première pierre. »
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
Et s’étant baissé de nouveau, il écrivait sur la terre.
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
Ayant entendu cette parole, [et se sentant repris par leur conscience, ] ils se retirèrent les uns après les autres, les plus âgés d’abord, [puis tous les autres, ] de sorte que Jésus resta seul avec la femme qui était au milieu.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
Alors Jésus s’étant relevé, et ne voyant plus que la femme, lui dit: « Femme, où sont ceux qui vous accusaient? Est-ce que personne ne vous a condamnée? »
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
Elle répondit: « Personne, Seigneur »; Jésus lui dit: « Je ne vous condamne pas non plus. Allez, et ne péchez plus. »
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
Jésus leur parla de nouveau, disant: « Je suis la lumière du monde. Celui qui me suit ne marchera pas dans les ténèbres, mais il aura la lumière de la vie. »
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
Sur quoi les Pharisiens lui dirent: « Vous rendez témoignage de vous-même; votre témoignage n’est pas digne de foi. »
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jésus leur répondit: « Quoique je rende témoignage de moi-même, mon témoignage est véridique, parce que je sais d’où je suis venu et où je vais; mais vous, vous ne savez d’où je viens, ni ou je vais.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
Vous jugez selon la chair; moi je ne juge personne.
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
Et si je juge, mon jugement est véridique, car je ne suis pas seul, mais moi, et le Père qui m’a envoyé.
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
Il est écrit dans votre Loi, que le témoignage de deux hommes est digne de foi.
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
Or, je rends témoignage de moi-même, et le Père qui m’a envoyé rend aussi témoignage de moi. »
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
Ils lui dirent donc: « Où est votre Père? »Jésus répondit: « Vous ne connaissez ni moi, ni mon Père: si vous me connaissiez, vous connaîtriez aussi mon Père. »
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
Jésus parla de la sorte dans le parvis du Trésor, lorsqu’il enseignait dans le temple; et personne ne mit la main sur lui, parce que son heure n’était pas encore venue.
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
Jésus leur dit encore: « Je m’en vais, et vous me chercherez, et vous mourrez dans votre péché. Où je vais, vous ne pouvez venir. »
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
Les Juifs disaient donc: « Est-ce qu’il va se tuer lui-même, puisqu’il dit: Où je vais, vous ne pouvez venir? »
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
Et il leur dit: « Vous, vous êtes d’en bas, moi, je suis d’en haut; vous êtes de ce monde, moi, je ne suis pas de ce monde.
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
C’est pourquoi je vous ai dit que vous mourrez dans votre péché; car si vous ne croyez pas que je suis le Messie, vous mourrez dans votre péché. —
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
« Qui êtes-vous? » lui dirent-ils. Jésus leur répondit: « Absolument ce que je vous déclare.
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
J’ai beaucoup de choses à dire de vous et à condamner en vous, mais celui qui m’a envoyé est véridique, et ce que j’ai entendu de lui, je le dis au monde. »
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
Ils ne comprirent point qu’il leur parlait du Père.
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
Jésus donc leur dit: « Lorsque vous aurez élevé le Fils de l’homme, alors vous connaîtrez qui je suis, et que je ne fais rien de moi-même, mais que je dis ce que mon Père m’a enseigné.
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
Et celui qui m’a envoyé est avec moi, et il ne m’a pas laissé seul, parce que je fais toujours ce qui lui plaît. » —
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
Comme il disait ces choses, beaucoup crurent en lui.
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
Jésus dit donc aux Juifs qui avaient cru en lui: « Si vous demeurez dans ma parole, vous êtes vraiment mes disciples;
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
vous connaîtrez la vérité, et la vérité vous rendra libres. »
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
Il lui répondirent: « Nous sommes la race d’Abraham, et nous n’avons jamais été esclaves de personne; comment dites-vous: Vous deviendrez libres? »
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
Jésus leur répondit: « En vérité, en vérité, je vous le dis, quiconque se livre au péché est esclave du péché.
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
Or, l’esclave ne demeure pas toujours dans la maison; mais le fils y demeure toujours. (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
Si donc le Fils vous affranchit, vous serez vraiment libres.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
Je sais que vous êtes enfants d’Abraham; mais vous cherchez à me faire mourir, parce que ma parole ne pénètre pas en vous.
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
Moi je vous dis ce que j’ai vu chez mon Père; et vous, vous faites ce que vous avez vu chez votre père. »
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
Ils lui répondirent: « Notre père, c’est Abraham. » Jésus leur dit: « Si vous étiez enfants d’Abraham, vous feriez les œuvres d’Abraham.
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
Mais maintenant vous cherchez à me faire mourir, moi qui vous ai dit la vérité que j’ai entendue de Dieu: ce n’est point ce qu’a fait Abraham.
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
Vous faites les œuvres de votre père. » Ils lui dirent: « Nous ne sommes pas des enfants de fornication; nous avons un seul Père, qui est Dieu. »
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
Jésus leur dit: « Si Dieu était votre Père, vous m’aimeriez, car c’est de Dieu que je suis sorti et que je viens; et je ne suis pas venu de moi-même, mais c’est lui qui m’a envoyé.
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
Pourquoi ne reconnaissez-vous pas mon langage? Parce que vous ne pouvez entendre ma parole.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
Le père dont vous êtes issus, c’est le diable, et vous voulez accomplir les désirs de votre père. Il a été homicide dès le commencement, et n’est point demeuré dans la vérité, parce qu’il n’y a point de vérité en lui. Lorsqu’il profère le mensonge, il parle de son propre fonds; car il est menteur, et le père du mensonge.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
Et moi, parce que je vous dis la vérité, vous ne me croyez pas.
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
Qui de vous me convaincra de péché? Si je dis la vérité, pourquoi ne me croyez-vous pas?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
Celui qui est de Dieu entend la parole de Dieu; c’est parce que vous n’êtes pas de Dieu que vous ne l’entendez pas. »
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
Les Juifs lui répondirent: « N’avons-nous pas raison de dire que vous êtes un Samaritain et que vous êtes possédé d’un démon? »
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
Jésus répondit: « Il n’y a point en moi de démon; mais j’honore mon Père, et vous, vous m’outragez.
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
Pour moi, je n’ai pas souci de ma gloire: il est quelqu’un qui en prend soin et qui fera justice.
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
En vérité, en vérité, je vous le dis, si quelqu’un garde ma parole, il ne verra jamais la mort. » (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
Les Juifs lui dirent: « Nous voyons maintenant qu’un démon est en vous. Abraham est mort, les prophètes aussi, et vous, vous dites: Si quelqu’un garde ma parole, il ne verra jamais la mort. (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
Êtes-vous plus grand que notre père Abraham, qui est mort? Les Prophètes aussi sont morts; qui prétendez-vous être? »
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jésus répondit: « Si je me glorifie moi-même, ma gloire n’est rien; c’est mon Père qui me glorifie, lui dont vous dites qu’il est votre Dieu;
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
et pourtant vous ne le connaissez pas; mais moi, je le connais; et si je disais que je ne le connais pas, je serais menteur comme vous. Mais je le connais et je garde sa parole.
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Abraham votre père, a tressailli de joie de ce qu’il devait voir mon jour; il l’a vu, et il s’est réjoui. »
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
Les Juifs lui dirent: « Vous n’avez pas encore cinquante ans, et vous avez vu Abraham! »
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jésus leur répondit: « En vérité, en vérité, je vous le dis, avant qu’Abraham fût, je suis. »
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
Alors ils prirent des pierres pour les lui jeter; mais Jésus se cacha, et sortit du temple.

< Yohanna 8 >