< Yohanna 8 >
1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
mais Jésus s'est rendu sur le mont des Oliviers.
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
Or, de grand matin, il entra de nouveau dans le temple, et tout le peuple vint à lui. Il s'assit et les enseigna.
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
Les scribes et les pharisiens amenèrent une femme surprise en adultère. L'ayant placée au milieu,
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
ils lui dirent: Maître, nous avons trouvé cette femme adultère, en flagrant délit.
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
Or, dans notre loi, Moïse nous a ordonné de lapider de telles femmes. Que dis-tu donc d'elle? »
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
Ils dirent cela pour l'éprouver, afin d'avoir quelque chose à lui reprocher. Mais Jésus se baissa et écrivit sur la terre avec son doigt.
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
Comme ils continuaient à l'interroger, il leva les yeux et leur dit: « Que celui d'entre vous qui est sans péché lui jette la première pierre. »
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
De nouveau, il se baissa et écrivit sur la terre avec son doigt.
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
Ceux-ci, après avoir entendu cela, convaincus par leur conscience, sortirent un par un, depuis le plus âgé jusqu'au dernier. Jésus resta seul avec la femme, là où elle était, au milieu.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
Jésus, s'étant levé, la vit et dit: « Femme, où sont tes accusateurs? Personne ne t'a condamnée? »
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
Elle a dit: « Personne, Seigneur. » Jésus a dit: « Je ne te condamne pas non plus. Va ton chemin. Désormais, ne pèche plus. »
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
Jésus leur parla de nouveau, en disant: « Je suis la lumière du monde. Celui qui me suit ne marchera pas dans les ténèbres, mais il aura la lumière de la vie. »
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
Les pharisiens lui dirent donc: « Tu témoignes de toi-même. Ton témoignage n'est pas valable. »
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jésus leur répondit: « Même si je rends témoignage de moi-même, mon témoignage est vrai, car je sais d'où je viens et où je vais; mais vous, vous ne savez ni d'où je viens ni où je vais.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
Vous jugez selon la chair. Moi, je ne juge personne.
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
Et quand bien même je jugerais, mon jugement est vrai, car je ne suis pas seul, mais je suis avec le Père qui m'a envoyé.
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
Il est aussi écrit dans votre loi que le témoignage de deux personnes est valable.
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
Moi, je suis celui qui rend témoignage de moi-même, et le Père qui m'a envoyé rend témoignage de moi. »
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
Ils lui dirent donc: « Où est ton Père? » Jésus répondit: « Vous ne connaissez ni moi ni mon Père. Si vous me connaissiez, vous connaîtriez aussi mon Père. »
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
Jésus prononça ces paroles dans le trésor, comme il enseignait dans le temple. Et personne ne l'arrêta, parce que son heure n'était pas encore venue.
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
Jésus leur dit donc encore: « Je m'en vais, et vous me chercherez, et vous mourrez dans vos péchés. Là où je vais, vous ne pouvez pas venir. »
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
Les Juifs dirent donc: « Se tuera-t-il, parce qu'il dit: « Où je vais, vous ne pouvez pas venir »? »
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
Il leur dit: « Vous êtes d'en bas. Moi, je suis d'en haut. Vous êtes de ce monde. Je ne suis pas de ce monde.
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
Je vous ai donc dit que vous mourrez dans vos péchés; car si vous ne croyez pas que je suis lui, vous mourrez dans vos péchés. »
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
Ils lui dirent donc: « Qui es-tu? » Jésus leur dit: « Ce que je vous dis depuis le commencement.
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
J'ai beaucoup de choses à dire et à juger à votre sujet. Mais celui qui m'a envoyé est vrai; et ce que j'ai entendu de lui, je le dis au monde entier. »
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
Ils ne comprenaient pas qu'il leur parlait du Père.
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
Jésus leur dit donc: « Quand vous aurez élevé le Fils de l'homme, vous saurez que c'est moi, et je ne fais rien de moi-même; mais c'est comme mon Père me l'a enseigné que je dis ces choses.
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
Celui qui m'a envoyé est avec moi. Le Père ne m'a pas laissé seul, car je fais toujours ce qui lui est agréable. »
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
Comme il parlait ainsi, beaucoup crurent en lui.
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
Jésus dit donc aux Juifs qui avaient cru en lui: « Si vous demeurez dans ma parole, vous êtes vraiment mes disciples.
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
Vous connaîtrez la vérité, et la vérité vous rendra libres. »
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
Ils lui répondirent: « Nous sommes la descendance d'Abraham, et nous n'avons jamais été asservis à personne. Comment peux-tu dire: « Vous serez libérés »? »
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
Jésus leur répondit: Je vous le dis en vérité, quiconque commet un péché est esclave du péché.
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn )
Un esclave ne demeure pas toujours dans la maison. Un fils demeure pour toujours. (aiōn )
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
Si donc le Fils vous rend libres, vous serez vraiment libres.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
Je sais que vous êtes la postérité d'Abraham, et pourtant vous cherchez à me tuer, parce que ma parole ne trouve pas de place en vous.
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
Je dis les choses que j'ai vues avec mon Père; et vous aussi, vous faites les choses que vous avez vues avec votre père. »
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
Ils lui répondirent: « Notre père est Abraham. » Jésus leur dit: « Si vous étiez les enfants d'Abraham, vous feriez les œuvres d'Abraham.
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
Mais maintenant vous cherchez à me tuer, moi qui vous ai dit la vérité que j'ai entendue de Dieu. Ce n'est pas Abraham qui a fait cela.
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
Vous faites les œuvres de votre père. » Ils lui dirent: « Nous ne sommes pas nés de l'immoralité sexuelle. Nous avons un seul Père, Dieu. »
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
C'est pourquoi Jésus leur dit: « Si Dieu était votre père, vous m'aimeriez, car je suis sorti et je suis venu de Dieu. Car je ne suis pas venu de moi-même, mais c'est lui qui m'a envoyé.
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
Pourquoi ne comprenez-vous pas ma parole? Parce que vous n'entendez pas ma parole.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
Vous êtes de votre père le diable, et vous voulez faire les désirs de votre père. Il a été meurtrier dès le commencement, et il ne tient pas dans la vérité, parce qu'il n'y a pas de vérité en lui. Quand il dit un mensonge, il parle de lui-même, car il est menteur et père du mensonge.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
Mais parce que je dis la vérité, vous ne me croyez pas.
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
Lequel d'entre vous me convainc de péché? Si je dis la vérité, pourquoi ne me croyez-vous pas?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
Celui qui est de Dieu entend les paroles de Dieu. C'est pourquoi vous n'entendez pas, parce que vous n'êtes pas de Dieu. »
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
Alors les Juifs lui répondirent: « Ne disons-nous pas bien que tu es un Samaritain, et que tu as un démon? »
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
Jésus répondit: « Je n'ai pas de démon, mais j'honore mon Père et vous me déshonorez.
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
Mais je ne cherche pas ma propre gloire. Il y a quelqu'un qui cherche et qui juge.
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn )
En vérité, je vous le dis, si quelqu'un garde ma parole, il ne verra jamais la mort. » (aiōn )
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn )
Alors les Juifs lui dirent: « Nous savons maintenant que tu as un démon. Abraham est mort, ainsi que les prophètes; et toi, tu dis: « Si quelqu'un garde ma parole, il ne goûtera jamais à la mort. (aiōn )
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
Es-tu plus grand que notre père Abraham, qui est mort? Les prophètes sont morts. Pour qui te prends-tu? »
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jésus répondit: « Si je me glorifie moi-même, ma gloire n'est rien. C'est mon Père qui me glorifie, lui dont vous dites qu'il est notre Dieu.
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
Vous ne l'avez pas connu, mais moi, je le connais. Si je disais: « Je ne le connais pas », je serais comme vous, un menteur. Mais moi, je le connais et je garde sa parole.
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Ton père Abraham s'est réjoui de voir mon jour. Il l'a vu et s'est réjoui. »
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
Les Juifs lui dirent donc: « Tu n'as pas encore cinquante ans! As-tu vu Abraham? »
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jésus leur dit: « En vérité, je vous le dis, avant qu'Abraham n'existe, JE SUIS. »
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
Ils prirent donc des pierres pour les jeter contre lui, mais Jésus se cacha et sortit du temple, après avoir traversé le milieu d'eux, et il passa ainsi.