< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
And at dawn he came again to the temple,
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
and all the people were coming unto him, and having sat down, he was teaching them;
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
and the scribes and the Pharisees bring unto him a woman having been taken in adultery, and having set her in the midst,
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
they say to him, 'Teacher, this woman was taken in the very crime — committing adultery,
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
and in the law, Moses did command us that such be stoned; thou, therefore, what dost thou say?'
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
and this they said, trying him, that they might have to accuse him. And Jesus, having stooped down, with the finger he was writing on the ground,
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
and when they continued asking him, having bent himself back, he said unto them, 'The sinless of you — let him first cast the stone at her;'
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
and again having stooped down, he was writing on the ground,
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
and they having heard, and by the conscience being convicted, were going forth one by one, having begun from the elders — unto the last; and Jesus was left alone, and the woman standing in the midst.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
And Jesus having bent himself back, and having seen no one but the woman, said to her, 'Woman, where are those — thine accusers? did no one pass sentence upon thee?'
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
and she said, 'No one, Sir;' and Jesus said to her, 'Neither do I pass sentence on thee; be going on, and no more sin.'
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
Again, therefore, Jesus spake to them, saying, 'I am the light of the world; he who is following me shall not walk in the darkness, but he shall have the light of the life.'
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
The Pharisees, therefore, said to him, 'Thou of thyself dost testify, thy testimony is not true;'
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jesus answered and said to them, 'And if I testify of myself — my testimony is true, because I have known whence I came, and whither I go, and ye — ye have not known whence I come, or whither I go.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
'Ye according to the flesh do judge; I do not judge any one,
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
and even if I do judge my judgment is true, because I am not alone, but I and the Father who sent me;
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
and also in your law it hath been written, that the testimony of two men are true;
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
I am [one] who is testifying of myself, and the Father who sent me doth testify of me.'
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
They said, therefore, to him, 'Where is thy father?' Jesus answered, 'Ye have neither known me nor my Father: if me ye had known, my Father also ye had known.'
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
These sayings spake Jesus in the treasury, teaching in the temple, and no one seized him, because his hour had not yet come;
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
therefore said Jesus again to them, 'I go away, and ye will seek me, and in your sin ye shall die; whither I go away, ye are not able to come.'
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
The Jews, therefore, said, 'Will he kill himself, because he saith, Whither I go away, ye are not able to come?'
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
and he said to them, 'Ye are from beneath, I am from above; ye are of this world, I am not of this world;
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
I said, therefore, to you, that ye shall die in your sins, for if ye may not believe that I am [he], ye shall die in your sins.'
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
They said, therefore, to him, 'Thou — who art thou?' and Jesus said to them, 'Even what I did speak of to you at the beginning;
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
many things I have to speak concerning you and to judge, but He who sent me is true, and I — what things I heard from Him — these I say to the world.'
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
They knew not that of the Father he spake to them;
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
Jesus, therefore, said to them, 'When ye may lift up the Son of Man then ye will know that I am [he]; and of myself I do nothing, but according as my Father did teach me, these things I speak;
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
and He who sent me is with me; the Father did not leave me alone, because I, the things pleasing to Him, do always.'
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
As he is speaking these things, many believed in him;
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
Jesus, therefore, said unto the Jews who believed in him, 'If ye may remain in my word, truly my disciples ye are, and ye shall know the truth,
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
and the truth shall make you free.'
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
They answered him, 'Seed of Abraham we are; and to no one have we been servants at any time; how dost thou say — Ye shall become free?'
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
Jesus answered them, 'Verily, verily, I say to you — Every one who is committing sin, is a servant of the sin,
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
and the servant doth not remain in the house — to the age, the son doth remain — to the age; (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
if then the son may make you free, in reality ye shall be free.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
'I have known that ye are seed of Abraham, but ye seek to kill me, because my word hath no place in you;
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
I — that which I have seen with my Father do speak, and ye, therefore, that which ye have seen with your father — ye do.'
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
They answered and said to him, 'Our father is Abraham;' Jesus saith to them, 'If children of Abraham ye were, the works of Abraham ye were doing;
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
and now, ye seek to kill me — a man who hath spoken to you the truth I heard from God; this Abraham did not;
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
ye do the works of your father.' They said, therefore, to him, 'We of whoredom have not been born; one Father we have — God;'
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
Jesus then said to them, 'If God were your father, ye were loving me, for I came forth from God, and am come; for neither have I come of myself, but He sent me;
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
wherefore do ye not know my speech? because ye are not able to hear my word.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
'Ye are of a father — the devil, and the desires of your father ye will to do; he was a man-slayer from the beginning, and in the truth he hath not stood, because there is no truth in him; when one may speak the falsehood, of his own he speaketh, because he is a liar — also his father.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
'And because I say the truth, ye do not believe me.
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
Who of you doth convict me of sin? and if I speak truth, wherefore do ye not believe me?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
he who is of God, the sayings of God he doth hear; because of this ye do not hear, because of God ye are not.'
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
The Jews, therefore, answered and said to him, 'Do we not say well, that thou art a Samaritan, and hast a demon?'
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
Jesus answered, 'I have not a demon, but I honour my Father, and ye dishonour me;
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
and I do not seek my own glory; there is who is seeking and is judging;
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
verily, verily, I say to you, If any one may keep my word, death he may not see — to the age.' (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
The Jews, therefore, said to him, 'Now we have known that thou hast a demon; Abraham did die, and the prophets, and thou dost say, If any one may keep my word, he shall not taste of death — to the age! (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
Art thou greater than our father Abraham, who died? and the prophets died; whom dost thou make thyself?'
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jesus answered, 'If I glorify myself, my glory is nothing; it is my Father who is glorifying me, of whom ye say that He is your God;
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
and ye have not known Him, and I have known Him, and if I say that I have not known Him, I shall be like you — speaking falsely; but I have known Him, and His word I keep;
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Abraham, your father, was glad that he might see my day; and he saw, and did rejoice.'
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
The Jews, therefore, said unto him, 'Thou art not yet fifty years old, and Abraham hast thou seen?'
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jesus said to them, 'Verily, verily, I say to you, Before Abraham's coming — I am;'
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
they took up, therefore, stones that they may cast at him, but Jesus hid himself, and went forth out of the temple, going through the midst of them, and so passed by.

< Yohanna 8 >