< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
But Jesus went [with us disciples] to Olive [Tree] Hill [and we stayed near there that night].
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
Early the next morning, we returned to the Temple [courtyard]. Many people gathered around Jesus, so he sat down to teach them.
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
Then men who taught the [Jewish] laws and some of [SYN] the Pharisee [religious group] brought a woman to him. She was seized {[They] had [arranged to] seize her} while she was having sex with a man who was not her husband. They made her stand up in front of the group [that was listening to Jesus].
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
Then they said to Jesus, “Teacher, this woman was seized {[we] seized this woman} while she was having sex with a man who is not her husband.
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
Moses commanded us in the laws that [he gave us] that we should throw stones at such women [and kill them]. So what do you say [we should do]?”
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
They asked this question as a trap so that they could accuse him. [If he said that they should not kill her, they would shame him for disobeying the law of Moses. If he said that they should kill her, they could accuse him to the Roman governor]. But Jesus bent down and wrote something on the ground with his finger.
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
While they continued to question him, he stood up and said to them, “Whichever one of you has never sinned can be the first one to start throwing stones at her.”
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
Then he stooped down and wrote [some more] on the ground.
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
After they heard what he said, those [who were questioning him] went away, one by one, the older ones first [and then the younger ones, knowing they were all sinners]. Finally only Jesus was there, along with the woman.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
Jesus stood up and asked her, “Woman, where are they? Has no one said you must die for your sin?”
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
She said, “No, sir, no one.” Then Jesus said, “I do not condemn you either. Go [home] now, and do not continue your sinful [life] any longer!”]
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
Jesus spoke to the people again. He said, “I am [like] a light [MET] for [all the people in] [MTY] the world. [Just like a light reveals what has been in the darkness] [MET], [I reveal God’s truth to them]. Those who walk in the darkness [are unaware of what is around them]. But those who become my disciples will always be aware [of God’s truth] [MET]. They will have my light [which shows them how to have eternal] life.”
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
So the Pharisees said to him, “You are just telling about yourself! [Since there is no one else to verify these things that you say about yourself], [we] do not [need to accept that] what you say is true.”
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jesus replied, “Even if I were the [only one to] say these things about myself, what I say is true, because I know that I came from [heaven], and I know that I am going [back to heaven]. But you do not know where I came from or where I am going.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
You judge people according to human standards. [The reason] that I am [here is] not (to condemn people/to say that I will punish people) [for their sins].
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
But if I did judge [people], what I decided would be correct, because I am not the [only] one [who will decide those things]. I and the one who sent me will both decide.
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
It is written {[Moses] wrote} in your law that if [at least] two people testify that [some event has happened], [people should consider] that what they say is true.
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
I am telling you about myself, and the other one who is telling you about me is [my] Father who sent me. [So you should believe that what we declare is true].”
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
Then they asked him, “[If you have a] father whom [we can question about you], where is he?” Jesus replied, “You do not know [who] I [really am]. If you knew who I [really am], you would know who my Father is also.”
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
He said these things when he was in the Temple [courtyard], near the place where the people put their offerings. [This was also very close to the place where the Jewish council met]. But no one seized him to arrest him, because it was not yet time [MTY] [for him to suffer and die].
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
Jesus also said to them, “I [will soon be] going away. Then [at the end of your life] you will seek me, but you will die [without God forgiving] your sins. Where I will go, you will not be able to come.”
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
So the Jewish [leaders] said among themselves, “Is he going to kill himself? Is that the reason that he said, ‘Where I go, you will not be able to come’?”
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
But Jesus continued by saying to them, “You were born here in this world, but I came from heaven. You belong to those who are opposed to God [MTY]. I do not belong to them.
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
I told you that you will die [without God forgiving] your sins. If you do not believe that I am [who I say that I am], you will die [without God forgiving] your sins.”
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
So they said to him, “You! Who do you think you are?” Jesus said to them, “Ever since I began [teaching], I have been telling you who I am!
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
I could judge you and say that [you are guilty of] many things. But instead, [I will say only] what the one who sent me tells me to say. [What he says] is true, and I tell the people in the world [MTY] what I have heard from him.”
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
They did not understand that he was talking about his Father [in heaven].
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
So Jesus said, “I am the one who came down from heaven, but when you lift me up [on a cross to kill me], you will know who I am. You will also know that I do not do anything with my own [authority]. Instead, I say just what [my] Father has taught me.
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
He is the one who sent me, and he helps me. Because I always do the things that please him, he has never abandoned me.”
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
As Jesus was saying these things, many people believed that he [was] ([from God/the Messiah]).
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
Then Jesus said to the Jews who now said they believed in him, “If you continue to [live in accordance with] my message, you will truly be my disciples.
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
Then you will know [God’s] truth, and as a result of [your believing his] truth, he [PRS] will free you [from being controlled by the one who has made you his slaves].”
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
They replied to him, “We are descendants of Abraham. We have never been anyone’s slaves. So why do you say [we will] be freed [from being someone’s slaves]?”
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
Jesus replied, “Listen carefully to what I am going to tell you. All those who continue to sin are [forced to obey] their sinful desires [MET], [just like] a slave [is forced to obey his master].
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
A slave is not a permanent member of a family. But a son is a member of a family forever. [Similarly, you say you are members of God’s family because you are descendants of Abraham, but really, because you are like slaves of your sinful desires, you are no longer permanent members of God’s family]. (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
So if you allow me to free you, you will truly be free.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
I know that you are Abraham’s descendants. But you are trying to kill me because [you are not] allowing [PRS] my message to continue [to change] your inner being.
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
I am telling you what I saw when I was with [my] Father. But you do the things that you have heard from your father.”
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
They replied to him, “Abraham is our ancestor.” Jesus said to them, “If you were Abraham’s descendants, [your character would be like Abraham’s character, and] you would do [good] things like Abraham did.
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
I have been telling you the truth that I heard from God, but you are trying to kill me. Abraham did not do things like that.
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
No! You are doing the things that your [real] father does.” They said to him, “[We do not know about you, but] we are not illegitimate children. And [spiritually], we have only one Father. That is God, and you do not know who your father is!”
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
Jesus said to them, “If God were your father, you would love me, because I came from God, and now I have come here [to this world]. My coming was not (because I [appointed] myself/with my own [authority]). He sent me.
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
(And I will tell you why you do not understand what I say./Do you know why you do not understand what I say?) [RHQ] It is because you do not want to accept my message.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
You belong to your father, (the devil/Satan), and you desire to do what he wants. He has [caused people to become] murderers from the time when [people] first [sinned]. He has abandoned [God’s] truth because he is a liar by his nature. Whenever he lies, he is speaking according to his [nature], because he is a liar and is the one who originates [MET] all lies.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
But because I tell you the truth, you do not believe me!
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
[Since I have never sinned], (none of you can show that I have sinned./can anyone among you show that I have sinned?) [RHQ] So, since I tell you the truth, (there is no good reason for your not believing me!/why is it that you do not believe me?) [RHQ]
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
Those who belong to God habitually obey God’s message. You do not belong to God, so you do not obey his message.”
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
The Jewish [leaders] [SYN] replied to him, “(We are certainly right by saying that you [believe what is false as] the Samaritans [do]!/Are we not right by saying that you [believe what is false as] the Samaritans [do]?) [RHQ] And that (a demon/an evil spirit) [controls] you!”
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
Jesus replied, “A demon does not [control] me! I honor my Father, and you do not honor me!
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
I am not trying to honor myself. There is someone else who desires [to honor me], and he is the one who will judge [whether it is I who am telling the truth or whether it is you who are telling the truth].
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
But the truth is that anyone who obeys what I say will never die!” (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
Then the Jewish [leaders] [SYN], [thinking that he was talking about ordinary death and not about spiritual death], said to him, “Now we are sure that a demon [controls] you! Abraham and the prophets died [long ago]! But you say that anyone who obeys what you teach will never die! (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
(You are certainly not greater than our ancestor Abraham!/Do you think you are greater than our ancestor Abraham?) [RHQ] He died, and all the prophets died, so who do you think you are [by saying something like that]?”
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jesus replied, “If I were honoring myself, that would be worthless. My Father is the one who you say is your God. He is the one who honors me.
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
Although you do not know him, I know him [and have a close relationship with him]. If I said that I did not know him, I would be a liar like you are. But I know him, and I obey what he says.
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Your ancestor Abraham was happy when he thought about what I would [do during] my life [MTY]. [It was as though] he saw that, and was happy.”
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
Then the Jewish [leaders] [SYN] said to him, “You are not 50 years old yet! So (you certainly did not see him!/how could you have seen him?) [RHQ] [Because he died long ago]!”
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jesus said to them, “The truth is that I existed before Abraham was born!”
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
So, [because they were very angry about Jesus thus saying that he] ([had eternally existed/was equal with God]), they picked up stones to throw at him [to kill him]. But [Jesus] caused them not to be able to see him, and he left the Temple courtyard.

< Yohanna 8 >