< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
But Jesus went to the Mount of Olives.
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
Early in the morning he again went to the temple courts. All the people came, and he sat down and taught them.
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
Then the scribes and the Pharisees brought him a woman who had been caught in adultery. Making her stand before them all,
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
they said to Jesus, testing him, “Teacher, this woman was caught in the very act of committing adultery.
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
In the law, Moses commanded us that such women should be stoned; what then do yoʋ say?”
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
(They said this to test him, so that they might have something to accuse him of.) But Jesus stooped down and wrote with his finger on the ground, taking no notice.
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
When they continued asking him, he stood up and said to them, “Let him among you who is without sin throw the first stone at her.”
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
And again he stooped down and wrote on the ground.
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
When they heard this, they were convicted by their own consciences and began to go away one by one, starting with the older men. So Jesus was left alone, with the woman there before him.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
Then Jesus stood up and saw no one but the woman. So he said to her, “Where are yoʋr accusers? Has no one condemned yoʋ?”
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
She said, “No one, Lord.” Jesus said, “Neither do I pass judgment on yoʋ; go and sin no more.”
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
Then Jesus spoke to them again, saying, “I am the light of the world. Whoever follows me will certainly not walk in darkness, but will have the light of life.”
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
So the Pharisees said to him, “Yoʋ are testifying about yoʋrself, so yoʋr testimony is not valid.”
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jesus answered them, “Even if I testify about myself, my testimony is valid, for I know where I came from and where I am going, but you do not know where I come from or where I am going.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
You judge according to the flesh, but I judge no one.
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
Yet even if I do judge, my judgment is valid; for I am not alone, but I am with the Father who sent me.
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
In your own law it is written that the testimony of two men is valid.
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
I testify about myself, and the Father who sent me also testifies about me.”
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
Then they said to him, “Where is yoʋr father?” Jesus answered, “You neither know me nor my Father. If you knew me, you would know my Father as well.”
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
(Jesus spoke these words in the treasury as he taught in the temple courts. But no one arrested him, because his hour had not yet come.)
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
Then Jesus said to them again, “I am going away, and you will seek me, but you will die in your sin. Where I am going, you cannot come.”
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
So the Jews said, “Is he going to kill himself? Is that what he means by saying, ‘Where I am going, you cannot come’?”
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
He said to them, “You are from below; I am from above. You are of this world; I am not of this world.
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
Therefore I said to you that you will die in your sins, for if you do not believe that I am he, you will die in your sins.”
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
They said to him, “Who are yoʋ?” Jesus said to them, “Exactly what I have been saying to you from the beginning.
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
I have many things to say about you and to judge, but he who sent me is true, and I tell the world what I have heard from him.”
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
(They did not know that he was speaking to them about the Father.)
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
So Jesus said to them, “When you lift up the Son of Man, then you will know that I am he and that I do nothing on my own authority, but I speak these things just as my Father taught me.
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
He who sent me is with me. The Father has not left me alone, for I always do what pleases him.”
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
As he was saying these things, many believed in him.
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
Then Jesus said to the Jews who had believed in him, “If you abide in my word, you are truly my disciples.
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
Then you will know the truth, and the truth will set you free.”
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
They answered him, “We are descendants of Abraham, and we have never been enslaved to anyone. How then can yoʋ say, ‘You will be set free’?”
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
Jesus answered them, “Truly, truly, I say to you, everyone who commits sin is a slave of sin.
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
The slave does not abide in the house forever; the son abides forever. (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
So if the son sets you free, you will be free indeed.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
I know that you are Abraham's descendants, but you are seeking to kill me because your hearts have no room for my word.
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
I speak of what I have seen with my Father; so you also are doing what you have seen with your father.”
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
They answered him, “Our father is Abraham.” Jesus said to them, “If you were children of Abraham, you would be doing the works of Abraham.
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
But now you are seeking to kill me, a man who has spoken to you the truth I heard from God. Abraham did not do such a thing.
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
You are doing the works of your father.” They said to him, “We were not born of fornication. We have one Father—God.”
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
Jesus said to them, “If God were your Father, you would love me, for I have come here from God. I have not come of my own accord, but he sent me.
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
Why do you not understand what I am saying? It is because you cannot bear to accept my word.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
You belong to your father the devil, and you want to carry out your father's desires. He was a murderer from the beginning and does not stand in the truth, because there is no truth in him. When he speaks lies, he speaks from his own character, because he is a liar and the father of lies.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
But because I speak the truth, you do not believe me.
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
Which one of you convicts me of sin? If I am telling the truth, why do you not believe me?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
Whoever belongs to God hears the words of God. The reason you do not hear them is because you do not belong to God.”
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
The Jews answered him, “Do we not rightly say that yoʋ are a Samaritan and have a demon?”
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
Jesus answered, “I do not have a demon, but I honor my Father, and you dishonor me.
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
I do not seek my own glory; there is one who seeks it, and he is the judge.
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
Truly, truly, I say to you, if anyone keeps my word, he will certainly never see death.” (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
The Jews said to him, “Now we know that yoʋ have a demon. Abraham died, and so did the prophets, yet yoʋ say, ‘If anyone keeps my word, he will certainly never taste death.’ (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
Are yoʋ greater than our father Abraham, who died? The prophets also died. Who do yoʋ make yoʋrself out to be?”
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jesus answered, “If I glorify myself, my glory is nothing. It is my Father who glorifies me, of whom you say, ‘He is our God.’
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
You do not know him, but I know him. If I were to say that I do not know him, I would be a liar like you. But I do know him, and I keep his word.
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Your father Abraham was glad that he would see my day. He saw it and rejoiced.”
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
Then the Jews said to him, “Yoʋ are not yet fifty years old, and yoʋ have seen Abraham?”
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jesus said to them, “Truly, truly, I say to you, before Abraham was, I am.”
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
So they picked up stones to throw at him, but Jesus hid himself and went out from the temple grounds. And passing through the crowd, he walked away.

< Yohanna 8 >