< Yohanna 8 >
1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
And Jesus went to the mount of Olives.
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
And in the morning he came again to the temple; and all the people came to him, and he sat down and taught them.
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
And the Scribes and Pharisees brought forward a woman that was caught in adultery. And when they had placed her in the midst,
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
they say to him: Teacher, this woman was caught openly in the act of adultery.
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
And in the law of Moses, God hath commanded us to stone such persons. What therefore dost thou say?
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
And this they said, tempting him, so that they might have ground to accuse him. But Jesus having stooped down, was writing on the ground.
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
And as they continued asking him, he straightened himself up, and said to them: Whoever among you is without sin, let him first cast a stone at her.
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
And, having again stooped down, he wrote on the ground.
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
And they, when they heard it, went out one by one, beginning with the older; and the woman was left, alone where she had stood in the midst.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
And when Jesus had straightened himself up, he said to the woman: Where are they? Doth no one condemn thee?
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
And she said: No man, Lord. And Jesus said: Neither do I condemn thee. Go thou, and henceforth sin no more.
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
And Jesus again conversed with them, and said: I am the light of the world: he that cometh to me, will not walk in darkness; but will find for himself the light of life.
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
The Pharisees said to him: Thou bearest witness of thyself, thy testimony is not certain.
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jesus answered and said to them: Although I bear witness of myself, my testimony is certain, because I know whence I came, and whither I go. But ye do not know, whence I came, and whither I go.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
Ye judge according to the flesh: I judge no one.
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
Yet if I Judge, my judgment is certain, because I am not alone, but I and my Father who sent me.
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
And in your law it is written, that the testimony of two persons is certain.
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
I am one: who bear witness of myself, and my Father who sent me, beareth witness of me.
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
They say to him: Where is thy Father? Jesus replied, and said to them: Ye neither know me nor my Father. If ye had known me, ye would also have known my Father.
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
These words spake Jesus in the treasury, as he taught in the temple: and no one laid hands on him, because his hour was not yet come.
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
Again Jesus said to them: I go away, and ye will seek me, and will die in your sins. And whither I go, ye cannot come.
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
The Jews said: Is he about to kill himself, that he should say, Whither I go ye cannot come?
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
And he said to them: Ye are from below, I am from above; ye are of this world, I am not of this world
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
I said to you, That ye will die in your sins; for if ye believe not that I am he, ye will die in your sins.
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
The Jews said to him: Who art thou? Jesus said to them: Although I have begun to converse with you,
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
I have yet many things to say and to Judge concerning you. But he that sent me is true: and the things which I have heard from him, them I speak in the world.
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
And they did not know, that he spake to them of the Father.
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
Jesus said to them again: When ye shall have lifted up the Son of man, then will ye know that I am he, and that I do nothing from my own pleasure, but as my Father taught me, so I speak.
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
And he that sent me, is with me; and my Father hath not left me alone, because I do, at all times, that which pleaseth him.
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
And when he had spoken these things, many believed on him.
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
And Jesus said to those Jews who believed on him: If ye continue in my word, ye will be truly my disciples.
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
And ye will know the truth; and the truth will make you free.
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
They say to him: We are the seed of Abraham, and never were in servitude to any man; and how sayest thou, Ye will be freemen?
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
Jesus said to them: Verily, verily, I say to you, That whoever committeth sin, is the servant of sin.
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn )
And a servant abideth not for ever in the house; but the Son abideth for ever. (aiōn )
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
If therefore the Son shall make you free, ye will really be free men.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
I know that ye are the children of Abraham; but ye seek to kill me, because ye do not acquiesce in my word.
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
I speak that which I have seen with my Father, and ye do that which ye have seen with your father.
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
They answered, and said to him: Our father is Abraham. Jesus said to them: If ye were children of Abraham, ye would do the works of Abraham.
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
But now ye seek to kill me, a man who hath told you the truth, which I have heard from God: this did not Abraham.
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
But ye do the works of your father. They say to him: We are not the offspring of whoredom; we have one Father, God.
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
Jesus said to them: If God were your Father, ye would love me; for I proceeded and came from God: I did not come of my own accord, but he sent me.
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
Why do ye not understand my speech? It is because ye cannot hear my speech.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
Ye are of your father, the calumniator; and the lust of your father ye are disposed to do. He was from the beginning a manslayer, and abode not in the truth; for the truth is not in him, and when he speaketh a lie he speaketh from himself, for he is a liar, and the father of it.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
But me, because I speak the truth, ye believe me not.
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
Which of you convicteth me of sin? And if I speak the truth, why do ye not believe me?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
He that is of God, heareth the words of God. Therefore ye do not hear, because ye are not of God.
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
The Jews answered, and said to him: Did we not well say, that thou art a Samaritan, and hast a demon?
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
Jesus said to them: I have no demon: but I honor God; and ye contemn me.
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
But I seek not my own glory: there is one that seeketh it, and judgeth.
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn )
Verily, verily, I say to you: He that keepeth my word, will never see death. (aiōn )
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn )
The Jews say to him: Now we know, that thou hast a demon. Abraham is dead, and the prophets; yet thou sayest: He that keepeth my word, will never taste death. (aiōn )
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
Art thou greater than our father Abraham who is dead, or than the prophets who died? What dost thou make thyself?
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jesus said to them: If I glorify myself, my glory is nothing. It is my Father that glorifieth me, of whom ye say, He is our God.
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
And ye know him not. But I know him; and if I should say, I know him not, I should be a liar, like you: but I do know him, and I observe his word.
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Abraham your father desired to see my day: and he saw it, and rejoiced.
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
The Jews say to him: Thou art not yet fifty years old, and hast thou seen Abraham?
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jesus said to them: Verily, verily I say to you, That before Abraham existed, I was.
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
And they took up stones to stone him. But Jesus concealed himself, and went out of the temple, and passed along among them, and went away.