< Yohanna 7 >
1 Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
After that Iesus wet about in Galile and wolde not go about in Iewry for the Iewes sought to kill him.
2 Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
The Iewes tabernacle feast was at honde.
3 sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
His brethren therfore sayde vnto him: get ye hence and go into Iewry yt thy disciples maye se thy workes yt thou doest.
4 Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
For ther is no man yt doeth eny thing secretly and he him selfe seketh to be knowen. Yf thou do soche thinges shewe thy selfe to the worlde.
5 Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
For as yet his brethre beleved not in him.
6 Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
Then Iesus sayd vnto them: My tyme is not yet come youre tyme is all waye redy.
7 Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
The worlde canot hate you. Me it hateth: because I testify of it that the workes of it are evyll.
8 Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
Go ye vp vnto this feast. I will not go vp yet vnto this feast for my tyme is not yet full come.
9 Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
These wordes he sayde vnto them and abode still in Galile.
10 Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
But assone as his brethren were goone vp then went he also vp vnto the feast: not openly but as it were prevely.
11 A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
Then sought him the Iewes at ye feast and sayde: Where is he?
12 A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
And moche murmurynge was ther of him amonge the people. Some sayde: He is good. Wother sayde naye but he deceaveth the people.
13 Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
How be it no ma spake openly of him for feare of the Iewes
14 Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
In ye middes of the feast Iesus went vp into the temple and taught.
15 Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
And the Iewes marveylled sayinge: How knoweth he ye scriptures seynge yt he never learned?
16 Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
Iesus answered them and sayde: My doctrine is not myne: but his that sent me.
17 Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
If eny man will do his will he shall knowe of the doctrine whether it be of God or whether I speake of my selfe.
18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
He that speaketh of him selfe seketh his awne prayse. But he that seketh his prayse that sent him the same is true and no vnrightewesnes is in him.
19 Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
Dyd not Moses geve you a lawe and yet none of you kepeth ye lawe? Why goo ye aboute to kyll me?
20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
The people answered and sayde: thou hast the devyll: who goeth aboute to kyll the?
21 Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
Iesus answered and sayde to them: I have done one worke and ye all marvayle.
22 Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
Moses therfore gave vnto you circumcision: not because it is of Moses but of the fathers. And yet ye on the Saboth daye circumcise a man.
23 To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
If a man on the Saboth daye receave circumcision without breakinge of the lawe of Moses: disdayne ye at me because I have made a man every whit whoale on the saboth daye?
24 Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
Iudge not after the vtter aperaunce: but iudge rightewes iudgement.
25 A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
Then sayd some of them of Ierusalem: Is not this he who they goo aboute to kyll?
26 Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
Beholde he speaketh boldly and they saye nothinge to him. Do the rulars knowe in dede that this is very Christ?
27 Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
How be it we knowe this man whence he is: but when Christ cometh no man shall knowe whence he is.
28 Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
Then cryed Iesus in ye temple as he taught sayinge: ye knowe me and whence I am ye knowe. And yet I am not come of my selfe but he yt sent me is true whom ye knowe not.
29 amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
I knowe him: for I am of him and he hath sent me.
30 Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
Then they sought to take him: but no ma layde hondes on him because his tyme was not yet come.
31 Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
Many of the people beleved on him and sayde: when Christ cometh will he do moo miracles then this man hath done?
32 Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
The pharises hearde that the people murmured suche thinges about him. Wherfore ye pharises and hye prestes sent ministres forthe to take him.
33 Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
Then sayde Iesus vnto the: Yet am I a lytell whyle with you and then goo I vnto him that sent me.
34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
Ye shall seke me and shall not fynde me: and where I am thyther can ye not come.
35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
Then sayde the Iewes bitwene the selves: whyther will he goo that we shall not fynde him? Will he goo amonge the gentyls which are scattered all a broade and teache the gentyls?
36 Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
What maner of sayinge is this that he sayde: ye shall seke me and shall not fynde me: and where I am thyther can ye not come?
37 A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
In the last daye that great daye of the feaste Iesus stode and cryed sayinge: If eny man thyrst let him come vnto me and drinke.
38 Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
He that beleveth on me as sayeth the scripture out of his belly shall flowe ryvers of water of lyfe.
39 Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
This spak he of the sprete which they that beleved on him shuld receave. For the holy goost was not yet there because that Iesus was not yet glorifyed.
40 Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
Many of the people when they hearde this sayinge sayd: of a truth this is a prophet
41 Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
Other sayde: this is Christ. Some sayde: shall Christ come out of Galile?
42 Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
Sayeth not the scripture that Christ shall come of the seed of David: and out of the toune of Bethleem where David was?
43 Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
So was ther dissencion amonge the people aboute him.
44 Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
And some of them wolde have taken him: but no man layed hondes on him.
45 A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
Then came ye ministres to ye hye prestes and pharises. And they sayde vnto the: why have ye not brought him?
46 Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
The servautes answered never man spake as this man doeth.
47 Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
Then answered the the pharises: are ye also disceaved?
48 Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
Doth eny of the rulers or of the pharises beleve on him?
49 A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
But the comen people whiche knowe not ye lawe are cursed.
50 Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
Nicodemus sayde vnto them: He that came to Iesus by nyght and was one of them.
51 “Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
Doth oure lawe iudge eny man before it heare him and knowe what he hath done?
52 Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
They answered and sayde vnto him: arte thou also of Galile? Searche and loke for out of Galile aryseth no Prophet.
53 Sai kowannensu ya koma gidansa.
And every man went vnto his awne housse.