< Yohanna 7 >
1 Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
After these things Jesus walked in Galilee: for he would not walk in Jewry, because the Jews sought to kill him.
2 Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
Now the Jew's feast of tabernacles was at hand.
3 sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
His brethren therefore said unto him, Depart behind, and go into Judaea, that your disciples also may see the works that you do.
4 Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
For there is no man that does any thing in secret, and he himself seeks to be known openly. If you do these things, show yourself to the world.
5 Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
For neither did his brethren believe in him.
6 Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
Then Jesus said unto them, My time is not yet come: but your time is always ready.
7 Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
The world cannot hate you; but me it hates, because I testify of it, that the works thereof are evil.
8 Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
Go all of you up unto this feast: I go not up yet unto this feast: for my time is not yet full come.
9 Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
When he had said these words unto them, he abode still in Galilee.
10 Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
But when his brethren were gone up, then went he also up unto the feast, not openly, but as it were in secret.
11 A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
Then the Jews sought him at the feast, and said, Where is he?
12 A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
And there was much murmuring among the people concerning him: for some said, He is a good man: others said, Nay; but he deceives the people.
13 Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
Nevertheless no man spoke openly of him for fear of the Jews.
14 Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
Now about the midst of the feast Jesus went up into the temple, and taught.
15 Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
And the Jews marvelled, saying, How knows this man letters, having never learned?
16 Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
Jesus answered them, and said, My doctrine is not mine, but his that sent me.
17 Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
If any man will do his will, he shall know of the doctrine, whether it be of God, or whether I speak of myself.
18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
He that speaks of himself seeks his own glory: but he that seeks his glory that sent him, the same is true, and no unrighteousness is in him.
19 Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
Did not Moses give you the law, and yet none of you keeps the law? Why go all of you about to kill me?
20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
The people answered and said, You have a devil: who goes about to kill you?
21 Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
Jesus answered and said unto them, I have done one work, and all of you all marvel.
22 Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
Moses therefore gave unto you circumcision; (not because it is of Moses, but of the fathers; ) and all of you on the sabbath day circumcise a man.
23 To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
If a man on the sabbath day receive circumcision, that the law of Moses should not be broken; are all of you angry at me, because I have made a man everything whole on the sabbath day?
24 Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
Judge not according to the appearance, but judge righteous judgment.
25 A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
Then said some of them of Jerusalem, Is not this he, whom they seek to kill?
26 Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
But, lo, he speaks boldly, and they say nothing unto him. Do the rulers know indeed that this is the very Christ?
27 Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
Nevertheless we know this man whence he is: but when Christ comes, no man knows whence he is.
28 Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
Then cried Jesus in the temple as he taught, saying, All of you both know me, and all of you know whence I am: and I am not come of myself, but he that sent me is true, whom all of you know not.
29 amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
But I know him: for I am from him, and he has sent me.
30 Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
Then they sought to take him: but no man laid hands on him, because his hour was not yet come.
31 Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
And many of the people believed on him, and said, When Christ comes, will he do more miracles than these which this man has done?
32 Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
The Pharisees heard that the people murmured such things concerning him; and the Pharisees and the chief priests sent officers to take him.
33 Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
Then said Jesus unto them, Yet a little while am I with you, and then I go unto him that sent me.
34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
All of you shall seek me, and shall not find me: and where I am, thither all of you cannot come.
35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
Then said the Jews among themselves, Where will he go, that we shall not find him? will he go unto the dispersed among the Gentiles, and teach the Gentiles?
36 Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
What manner of saying (logos) is this that he said, All of you shall seek me, and shall not find me: and where I am, thither all of you cannot come?
37 A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
In the last day, that great day of the feast, Jesus stood and cried, saying, If any man thirst, let him come unto me, and drink.
38 Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
He that believes on me, as the scripture has said, out of his belly shall flow rivers of living water.
39 Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
(But this spoke he of the Spirit, (pneuma) which they that believe on him should receive: for the Holy Spirit (pneuma) was not yet given; because that Jesus was not yet glorified.)
40 Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
Many of the people therefore, when they heard this saying, (logos) said, Truthfully this is the Prophet.
41 Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
Others said, This is the Christ. But some said, Shall Christ come out of Galilee?
42 Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
Has not the scripture said, That Christ comes of the seed of David, and out of the town of Bethlehem, where David was?
43 Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
So there was a division among the people because of him.
44 Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
And some of them would have taken him; but no man laid hands on him.
45 A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
Then came the officers to the chief priests and Pharisees; and they said unto them, Why have all of you not brought him?
46 Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
The officers answered, Never man spoke like this man.
47 Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
Then answered them the Pharisees, Are all of you also deceived?
48 Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
Have any of the rulers or of the Pharisees believed on him?
49 A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
But this people who knows not the law are cursed.
50 Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
Nicodemus says unto them, (he that came to Jesus by night, being one of them, )
51 “Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
Does our law judge any man, before it hear him, and know what he does?
52 Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
They answered and said unto him, Are you also of Galilee? Search, and look: for out of Galilee arises no prophet.
53 Sai kowannensu ya koma gidansa.
And every man went unto his own house.