< Yohanna 7 >
1 Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
Derefter vandrede Jesus omkring i Galilæa; thi han vilde ikke vandre i Judæa, fordi Jøderne søgte at slaa ham ihjel.
2 Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
Men Jødernes Højtid, Løvsalsfesten, var nær.
3 sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
Da sagde hans Brødre til ham: „Drag bort herfra og gaa til Judæa, for at ogsaa dine Disciple kunne se dine Gerninger, som du gør.
4 Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
Thi ingen gør noget i Løndom, naar han selv ønsker at være aabenbar; dersom du gør dette, da vis dig for Verden!”
5 Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
Thi heller ikke hans Brødre troede paa ham.
6 Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
Da siger Jesus til dem: „Min Tid er endnu ikke kommen; men eders Tid er stedse for Haanden.
7 Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
Verden kan ikke hade eder; men mig hader den, fordi jeg vidner om den, at dens Gerninger ere onde.
8 Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
Drager I op til Højtiden; jeg drager endnu ikke op til denne Højtid, thi min Tid er endnu ikke fuldkommet.”
9 Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
Da han havde sagt dette til dem, blev han i Galilæa.
10 Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
Men da hans Brødre vare dragne op til Højtiden, da drog han ogsaa selv op, ikke aabenlyst, men lønligt.
11 A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
Da ledte Jøderne efter ham paa Højtiden og sagde: „Hvor er han?”
12 A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
Og der blev mumlet meget om ham iblandt Skarerne; nogle sagde: „Han er en god Mand;” men andre sagde: „Nej, han forfører Mængden.”
13 Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
Dog talte ingen frit om ham af Frygt for Jøderne.
14 Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
Men da det allerede var midt i Højtiden, gik Jesus op i Helligdommen og lærte.
15 Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
Jøderne undrede sig nu og sagde: „Hvorledes kan denne have Lærdom, da han ikke er oplært?”
16 Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
Da svarede Jesus dem og sagde: „Min Lære er ikke min, men hans, som sendte mig.
17 Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
Dersom nogen vil gøre hans Villie, skal han erkende, om Læren er fra Gud, eller jeg taler af mig selv.
18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
Den, som taler af sig selv, søger sin egen Ære; men den, som søger hans Ære, der sendte ham, han er sanddru, og der er ikke Uret i ham.
19 Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
Har ikke Moses givet eder Loven? Og ingen af eder holder Loven. Hvorfor søge I at slaa mig ihjel?”
20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
Mængden svarede: „Du er besat; hvem søger at slaa dig ihjel?”
21 Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
Jesus svarede og sagde til dem: „Een Gerning gjorde jeg, og I undre eder alle derover.
22 Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
Moses har givet eder Omskærelsen, (ikke at den er fra Moses, men fra Fædrene) og I omskære et Menneske paa en Sabbat.
23 To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
Dersom et Menneske faar Omskærelse paa en Sabbat, for at Mose Lov ikke skal brydes, ere I da vrede paa mig, fordi jeg har gjort et helt Menneske rask paa en Sabbat?
24 Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
Dømmer ikke efter Skinnet, men dømmer en retfærdig Dom!”
25 A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
Da sagde nogle af dem fra Jerusalem: „Er det ikke ham, som de søge at slaa ihjel?
26 Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
Og se, han taler frit, og de sige intet til ham; mon Raadsherrerne virkelig skulde have erkendt, at han er Kristus?
27 Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
Dog — vi vide, hvorfra denne er; men naar Kristus kommer, kender ingen, hvorfra han er.”
28 Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
Derfor raabte Jesus, idet han lærte i Helligdommen, og sagde: „Baade kende I mig og vide, hvorfra jeg er! Og af mig selv er jeg ikke kommen, men han, som sendte mig, er sand, han, hvem I ikke kende.
29 amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
Jeg kender ham; thi jeg er fra ham, og han har udsendt mig.”
30 Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
De søgte da at gribe ham; og ingen lagde Haand paa ham, thi hans Time var endnu ikke kommen.
31 Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
Men mange af Folket troede paa ham, og de sagde: „Naar Kristus kommer, mon han da skal gøre flere Tegn, end denne har gjort?”
32 Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
Farisæerne hørte, at Mængden mumlede dette om ham; og Ypperstepræsterne og Farisæerne sendte Tjenere ud for at gribe ham.
33 Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
Da sagde Jesus: „Endnu en liden Tid er jeg hos eder, saa gaar jeg bort til den, som sendte mig.
34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
I skulle lede efter mig og ikke finde mig, og der, hvor jeg er, kunne I ikke komme.”
35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
Da sagde Jøderne til hverandre: „Hvor vil han gaa hen, siden vi ikke skulle finde ham? Mon han vil gaa til dem, som ere adspredte iblandt Grækerne, og lære Grækerne?
36 Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
Hvad er det for et Ord, han siger: I skulle lede efter mig og ikke finde mig, og der, hvor jeg er, kunne I ikke komme?”
37 A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
Men paa den sidste, den store Højtidsdag stod Jesus og raabte og sagde: „Om nogen tørster, han komme til mig og drikke!
38 Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
Den, som tror paa mig, af hans Liv skal der, som Skriften har sagt, flyde levende Vandstrømme.”
39 Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
Men dette sagde han om den Aand, som de, der troede paa ham, skulde faa; thi den Helligaand var der ikke endnu, fordi Jesus endnu ikke var herliggjort.
40 Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
Nogle af Mængden, som hørte disse Ord, sagde nu: „Dette er sandelig Profeten.”
41 Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
Andre sagde: „Dette er Kristus;” men andre sagde: „Mon da Kristus kommer fra Galilæa?
42 Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
Har ikke Skriften sagt, at Kristus kommer af Davids Sæd og fra Bethlehem, den Landsby, hvor David var?”
43 Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
Saaledes blev der Splid iblandt Mængden om ham.
44 Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
Men nogle af dem vilde gribe ham; dog lagde ingen Haand paa ham.
45 A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
Tjenerne kom nu til Ypperstepræsterne og Farisæerne, og disse sagde til dem: „Hvorfor have I ikke ført ham herhen?”
46 Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
Tjenerne svarede: „Aldrig har noget Menneske talt saaledes som dette Menneske.”
47 Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
Da svarede Farisæerne dem: „Ere ogsaa I forførte?
48 Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
Mon nogen af Raadsherrerne har troet paa ham, eller nogen af Farisæerne?
49 A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
Men denne Hob, som ikke kender Loven, er forbandet.”
50 Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
Nikodemus, han, som var kommen til ham om Natten og var en af dem, sagde til dem:
51 “Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
„Mon vor Lov dømmer et Menneske, uden at man først forhører ham og faar at vide, hvad han gør?”
52 Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
De svarede og sagde til ham: „Er ogsaa du fra Galilæa? Ransag og se, at der ikke fremstaar nogen Profet fra Galilæa.”
53 Sai kowannensu ya koma gidansa.
[Og de gik hver til sit Hus.]