< Yohanna 7 >
1 Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
Nakon toga Isus je obilazio po Galileji; nije htio u Judeju jer su Židovi tražili da ga ubiju.
2 Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
Bijaše blizu židovski Blagdan sjenica.
3 sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
Rekoše mu stoga njegova braća: “Otiđi odavle i pođi u Judeju da i tvoji učenici vide djela što činiš.
4 Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
Ta tko želi biti javno poznat, ne čini ništa u tajnosti. Ako već činiš sve to, očituj se svijetu.”
5 Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
Jer ni braća njegova nisu vjerovala u njega.
6 Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
Reče im nato Isus: “Moje vrijeme još nije došlo, a za vas je vrijeme svagda pogodno.
7 Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
Vas svijet ne može mrziti, ali mene mrzi jer ja svjedočim protiv njega: da su mu djela opaka.
8 Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
Vi samo uziđite na blagdan. Ja još ne uzlazim na ovaj blagdan jer moje se vrijeme još nije ispunilo.”
9 Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
To im reče i ostade u Galileji.
10 Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
Ali pošto njegova braća uziđoše na blagdan, uziđe i on, ne javno, nego potajno.
11 A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
A Židovi su ga tražili o blagdanu pitajući: “Gdje je onaj?”
12 A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
I među mnoštvom o njemu se mnogo šaptalo. Jedni govorahu: “Dobar je!” Drugi pak: “Ne, nego zavodi narod.”
13 Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
Ipak nitko nije otvoreno govorio o njemu zbog straha od Židova.
14 Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
Usred blagdana uziđe Isus u Hram i stade naučavati.
15 Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
Židovi se u čudu pitahu: “Kako ovaj znade Pisma, a nije učio?”
16 Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
Nato im Isus odvrati: “Moj nauk nije moj, nego onoga koji me posla.
17 Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
Ako tko hoće vršiti volju njegovu, prepoznat će da li je taj nauk od Boga ili ja sam od sebe govorim.
18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
Tko sam od sebe govori, svoju slavu traži, a tko traži slavu onoga koji ga posla, taj je istinit i nema u njemu nepravednosti.
19 Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
Nije li vam Mojsije dao Zakon? Pa ipak nitko od vas ne vrši Zakona.” “Zašto tražite da me ubijete?”
20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
Odgovori mnoštvo: “Zloduha imaš! Tko traži da te ubije?”
21 Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
Uzvrati im Isus: “Jedno djelo učinih i svi se čudite.
22 Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
Mojsije vam dade obrezanje - ne, ono i nije od Mojsija, nego od otaca - i vi u subotu obrezujete čovjeka.
23 To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
Ako čovjek može primiti obrezanje u subotu da se ne prekrši Mojsijev zakon, zašto se ljutite na mene što sam svega čovjeka ozdravio u subotu?
24 Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
Ne sudite po vanjštini, nego sudite sudom pravednim!”
25 A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
Rekoše tada neki Jeruzalemci: “Nije li to onaj koga traže da ga ubiju?
26 Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
A evo, posve otvoreno govori i ništa mu ne kažu. Da nisu možda i glavari doista upoznali da je on Krist?
27 Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
Ali za njega znamo odakle je, a kad Krist dođe, nitko neće znati odakle je!”
28 Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
Nato Isus, koji je učio u Hramu, povika: “Da! Poznajete me i znate odakle sam! A ipak ja nisam došao sam od sebe: postoji jedan istiniti koji me posla. Njega vi ne znate.
29 amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
Ja ga znadem jer sam od njega i on me poslao.”
30 Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
Židovi su otad vrebali da ga uhvate. Ipak nitko ne stavi na nj ruke jer još nije bio došao njegov čas.
31 Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
A mnogi iz mnoštva povjerovaše u nj te govorahu: “Zar će Krist, kada dođe, činiti više znamenja nego što ih ovaj učini?”
32 Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
Dočuli farizeji da se to u mnoštvu o njemu šapće. Stoga glavari svećenički i farizeji poslaše stražare da ga uhvate.
33 Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
Tada Isus reče: “Još sam malo vremena s vama i odlazim onomu koji me posla.
34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
Tražit ćete me i nećete me naći; gdje sam ja, vi ne možete doći.”
35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
Rekoše nato Židovi među sobom: “Kamo to ovaj kani da ga mi nećemo naći? Da ne kani poći raseljenima među Grcima i naučavati Grke?
36 Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
Što li znači besjeda koju reče: 'Tražit ćete me i nećete me naći; gdje sam ja, vi ne možete doći'?”
37 A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
U posljednji, veliki dan blagdana Isus stade i povika: “Ako je tko žedan, neka dođe k meni! Neka pije
38 Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
koji vjeruje u mene! Kao što reče Pismo: 'Rijeke će žive vode poteći iz njegove utrobe!'”
39 Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
To reče o Duhu kojega su imali primiti oni što vjeruju u njega. Tada doista ne bijaše još došao Duh jer Isus nije bio proslavljen.
40 Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
Kad su neki iz naroda čuli te riječi, govorahu: “Ovo je uistinu Prorok.”
41 Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
Drugi govorahu: “Ovo je Krist.” A bilo ih je i koji su pitali: “Pa zar Krist dolazi iz Galileje?
42 Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
Ne kaže li Pismo da Krist dolazi iz potomstva Davidova, i to iz Betlehema, mjesta gdje bijaše David?”
43 Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
Tako je u narodu nastala podvojenost zbog njega.
44 Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
Neki ga čak htjedoše uhvatiti, ali nitko ne stavi na nj ruke.
45 A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
Dođoše dakle stražari glavarima svećeničkim i farizejima, a ovi im rekoše: “Zašto ga ne dovedoste?”
46 Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
Stražari odgovore: “Nikada nitko nije ovako govorio.”
47 Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
Nato će im farizeji: “Zar ste se i vi dali zavesti?
48 Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
Je li itko od glavara ili farizeja povjerovao u njega?
49 A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
Ali ta svjetina koja ne pozna Zakona - to je prokleto!”
50 Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
Kaže im Nikodem - onaj koji ono prije dođe k Isusu, a bijaše jedan od njih:
51 “Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
“Zar naš Zakon sudi čovjeku ako ga prije ne sasluša i ne dozna što čini?”
52 Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
Odgovoriše mu: “Da nisi i ti iz Galileje? Istraži pa ćeš vidjeti da iz Galileje ne ustaje prorok.”
53 Sai kowannensu ya koma gidansa.
I otiđoše svaki svojoj kući.