< Yohanna 6 >
1 Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
Po tem odide Jezus na oni kraj morja Galilejskega ali Tiberijskega.
2 sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
In šlo je za njim veliko ljudstva, ko so videli njegove čudeže, ki jih je delal na bolnikih.
3 Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
Jezus pa izide na goro, in tu je z učenci svojimi sedel.
4 Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
Bila ja pa blizu Velika noč, praznik Judovski.
5 Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
Povzdignivši torej Jezus očí, in videvši, da veliko ljudstva k njemu dohaja, reče Filipu: Kje bomo kupili kruha, da bodo tí jedli?
6 Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
(To je pa govoril, izkušajoč ga; kajti on je vedel, kaj bo storil.)
7 Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
Odgovorí mu Filip: Za dve sto grošev kruha jim ni dosti, da bi vsakteri od njih kaj malega dobil.
8 Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
Reče mu eden učencev njegovih Andrej brat Simona Petra:
9 “Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
En deček je tu, kteri ima pet hlebov ječmenovih in dve ribici; ali kaj je to med toliko?
10 Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
Jezus pa reče: Dajte, posadite ljudí. Bilo je pa veliko trave na tem mestu. In posadé se možjé, kakih pet tisoči na število.
11 Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
Tedaj Jezus vzeme hlebe, in zahvali, ter razdelí učencem, učenci pa tém, ki so sedeli: in ravno tako tudi od ribic, kolikor so hoteli.
12 Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
Ko so se pa nasitili, velí učencem svojim: Zberite ostanke koscev, da nič ne pogine.
13 Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
Ter zberó, in napolnijo dvanajst košev koscev od petih hlebov ječmenovih, ki so preostali od téh, ktere so bili pojedli.
14 Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
Ljudjé pa, ko so videli čudež, kterega je bil Jezus storil, govorili so: Ta je res prerok, kteri je imel priti na svet.
15 Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
Jezus torej, vedoč, da bodo prišli in ga zgrabili, da ga naredé za kralja, umakne se zopet na goro on sam.
16 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
Ko se je pa zvečerilo, snidejo učenci njegovi na morje.
17 inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
In stopivši v ladjo, šli so na oni kraj morja v Kapernaum. In uže se jo mračilo, in Jezus ni bil k njim prišel,
18 Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
In morje se je od velikega vetra vzdigalo.
19 Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
Odplavivši se pa kakih pet in dvajset ali trideset bežajev, ugledajo Jezusa, da hodi po morji, in se približuje ladji; in uplašijo se.
20 Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
On jim pa reče: Jaz sem; ne bojte se!
21 Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
In željno so ga vzeli v ladjo, in precej je bila ladja na zemlji, v ktero so šli.
22 Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
Drugi dan pa ljudstvo, ktero je stalo onkraj morja, ko je videlo, da ni bilo tam druge ladje, razen tiste ene, v ktero so bili stopili učenci njegovi, in da Jezus ni vstopil z učenci svojimi v ladjo, nego da so bili učenci njegovi sami odšli;
23 Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
(Prišle so pa druge ladje iz Tiberijade blizu mesta, kjer so bili jedli kruh, ko je Gospod zahvalil; )
24 Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
Ko je torej ljudstvo videlo, da Jezusa ni tu, in tudi učencev njegovih ne: stopijo tudi oni v ladje, in pridejo v Kapernaum, iskajoč Jezusa.
25 Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
In ko ga najdejo onkraj morja, rekó mu: Rabi, kedaj si prišel sem?
26 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
Odgovorí jim Jezus in reče: Resnično resnično vam pravim, iščete me, ne za to, ker ste videli čudeže, nego ker ste jedli hlebe in ste se nasitili.
27 Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
Trudite se, ne za jed, ktera mine, nego za jed, ktera ostane za večno življenje, ktero vam bo sin človečji dal: kajti tega je potrdil oče Bog. (aiōnios )
28 Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
Rekó mu torej: Kaj naj storimo, da bomo delali dela Božja?
29 Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
Odgovorí jim Jezus in reče: To je delo Božje, da verujete v tega, kterega je on poslal.
30 Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
Pa mu rekó: Kakošno znamenje nam pokazuješ, da bi videli in ti verovali? kaj delaš?
31 Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
Očetje naši so jedli mano v puščavi, kakor jo pisano: "Kruh z neba jim je dal jesti."
32 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
Pa jim Jezus reče: Resnično resnično vam pravim: Ni vam dal Mojzes kruha z neba; nego oče moj vam daje pravi kruh z neba.
33 Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
Kajti kruh Božji je ta, kteri shaja z neba, in daje življenje svetu.
34 Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
Rekó mu torej: Gospod, daj nam vsegdar tega kruha.
35 Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
Jezus jim pa reče: Jaz sem kruh življenja; kdor k meni dohaja, ne bo nikoli lačen, in kdor veruje v mé, ne bo nikoli ožejal.
36 Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
Ali povedal sem vam, da ste me tudi videli, in ne verujete.
37 Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
Vse, kar mi oče dá, pride k meni; in kdor pride k meni, ne bom ga izgnal ven:
38 Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
Kajti prišel sem z neba, ne da bi delal po svojej volji, nego po volji tega, kteri me je poslal.
39 Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
Volja očeta, kteri me je poslal, je pa ta, da od tega, kar mi je dal, ničesar ne izgubim, nego da to poslednji dan obudim.
40 Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
In volja tega, kteri me je poslal, je ta, da ima vsak, kdor vidi sina in veruje va-nj, večno življenje, in jaz ga bom obudil poslednji dan. (aiōnios )
41 Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
Tedaj so Judje godrnjali nad njim, da je rekel: Jaz sem kruh, kteri je prišel z neba.
42 Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
In govorili so: Kaj ni ta sin Jožefov, komur mi očeta in mater poznamo? Kako torej govorí ta: Z neba sem prišel!
43 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
Jezus pa odgovorí in jim reče: Ne godrnjajte med seboj!
44 Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
Nikdor ne more priti k meni, če ga oče, kteri me je poslal, ne privleče, in jaz ga bom obudil poslednji dan.
45 A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
Pisano je v prerokih: "In vsi bodo učeni od Boga." Kdorkoli je torej slišal od očeta in se je naučil, dohaja k meni;
46 Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
Ne da bi bil kdo očeta videl, razen tisti, kteri je od Boga: ta je videl Boga.
47 Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
Resnično resnično vam pravim: Kdor veruje v mé, ima večno življenje. (aiōnios )
49 Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
Očetje vaši so jedli mano v puščavi, in pomrli so.
50 Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
Ta je kruh, kteri shaja z neba: da kdor od njega jé, ne umre.
51 Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
Jaz sem živi kruh, kteri sem z neba prišel; če kdo jé od tega kruha, živel bo vekomaj. Kruh pa, kterega bom jaz dal, je telo moje, ktero bom jaz dal za življenje sveta. (aiōn )
52 Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
Judje so se pa prepirali med seboj, govoreč: Kako nam more ta dati telo jesti?
53 Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
Pa jim Jezus reče: Resnično resnično vam pravim: Če ne boste jedli telesa sina človečjega, in pili njegove krví, ne boste imeli življenja v sebi.
54 Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
Kdor jé moje telo, in pije mojo kri, ima večno življenje, in jaz ga bom obudil poslednji dan. (aiōnios )
55 Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
Kajti telo moje je prava jed, in kri moja je prava pijača.
56 Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
Kdor jé moje telo, in pije mojo kri, prebiva v meni, in jaz v njem.
57 Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
Kakor je mene poslal živi oče, in jaz za voljo očeta živim: tako bo tudi tisti, kteri mene jé, živel, za voljo mene.
58 Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
Ta je kruh, kteri je z neba prišel; ne kakor so očetje vaši jedli mano, in so pomrli; kdor ta kruh jé, živel bo vekomaj. (aiōn )
59 Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
To je povedal v shajališči, ko je učil v Kapernaumu.
60 Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
Veliko torej učencev njegovih, kteri so poslušali, reče: Trda je ta beseda; kdo jo more poslušati?
61 Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
Vedoč pa Jezus sam v sebi, da učenci njegovi godrnjajo nad tem, reče jim: To vas pohujšuje?
62 Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
Kaj pa, ko boste videli sina človečjega, da gre gor, kjer je poprej bil?
63 Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
Duh je to, kar oživlja, telo nič ne pomaga; besede, ktere vam jaz govorim, duh so in življenje so.
64 Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
So pa nekteri med vami, kteri ne verujejo. Jezus namreč je od začetka vedel, kteri so, da ne verujejo, in kdo je, kteri ga bo izdal.
65 Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
In pravil je: Za to sem vam rekel, da ne more nihče k meni priti, če mu ne bo dano od očeta mojega.
66 Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
Posihmal je veliko učencev njegovih zopet odšlo, in nič več niso ž njim hodili.
67 Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
Tedaj reče Jezus dvanajsterim: Ali hočete tudi vi oditi?
68 Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
Pa mu odgovorí Simon Peter: Gospod, h komu pojdemo? Besede večnega življenja imaš. (aiōnios )
69 Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
In mi smo verovali, in vémo, da si ti Kristus, sin živega Boga.
70 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
Odgovorí jim Jezus: Ali vas nisem jaz dvanajst izvolil, in eden od vas je hudič?
71 (Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)
Govoril je pa za Juda Simonovega Iškarijana: kajti ta ga je imel izdati, in bil je eden od dvanajsterih.